Leadership News Hausa:
2025-03-02@20:25:09 GMT

Bikin Bazara Na Sinawa Ya Zama Biki Na Al’ummar Duniya

Published: 29th, January 2025 GMT

Bikin Bazara Na Sinawa Ya Zama Biki Na Al’ummar Duniya

Bikin bazara shi ne biki mafi dadewa da muhimmanci a bukukuwan gargajiya na Sin. Kuma bikin na ci gaba da kara bazuwa da samun karbuwa a fadin duniya.

A kwanakin baya-bayan nan, kasashe da hukumomin kasa da kasa da dama sun gudanar da shirye-shirye da nune-nunen dake da alaka da bikin bazara, kuma jama’a a fadin duniya sun hadu domin a dama da su cikin bikin murnar sabuwar shekarar ta Sin.

A wannan lokaci, 1 bisa 5 na al’ummar duniya ne ke murnar bikin ta mabanbantan hanyoyi, lamarin da ya mayar da bikin bazara zuwa wata al’adar gargajiya ta duniya tare da inganta fahimta da abota tsakanin jama’ar dukkan kasashe.

Alkaluman Watsa Shirye-Shiryen Shagalin Bikin Bazara Na CMG Na 2025 Sun Kai Sabon Matsayi Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Gudanar Da Binciken Lafiya Kyauta A Karkarar Sudan Ta Kudu

Hakan ba ya rasa nasaba da yadda al’adar ta taba kowanne bangare na rayuwa da kuma sakonnin da take dauke da su kamar na kyautata zumuncin iyali da girmama manya da tausayawa yara, wanda abubuwa ne dake da saukin fahimta ga jama’ar dukkan kasashe. A lokacin guda, ta hanyar bikin bazara, duniya ta ga kasar Sin dunkulalliya mai bude kofa, haka kuma ta shaida nasarorin da kasar ta samu wajen zamanantar da kanta.

Sinawa na mika fatansu na ban kwana da tsohuwar shekara da maraba da sabuwa ga duniya ne ta hanyar bikin bazara. Bikin bazara ba na Sin ba ne kadai, na daukacin duniya ne. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: bikin bazara Bikin bazara

এছাড়াও পড়ুন:

Babban Sakataren MDD Ya Taya Musulmi Murnar Shiga Watan Ramadan

Sakatare janar na Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres na mika sakon gaisuwa a yayin da al’ummar Musulmi a fadin duniya suka fara gudanar da azumin watan Ramadan.

Ramadan yana kunshe da dabi’u na tausayi, tausayawa da karamci. Sannan dama ce ta sake haduwa da dangi da sauran al’umma.

Kazalika dama ce ta tuna wadanda ba su samu damar sake ganin watan ba. Ga duk wadanda suka samu ganin wannan lokaci mai tsarki cikin halin gudun hijira da tashin hankali, ina so in bayyana sakon tausayawa a gare su.

Ina goyon baya ga duk wadanda ke cikin halin tsanani da wahala, tun daga Gaza da sauran yankuna, zuwa Sudan, Sahel da sauran su. Kuma ina mai ba da hadin kai da masu gudanar da Azumin watan Ramadan da yin kira ga zaman lafiya da mutunta juna. A duk watan Ramadan, na kan kai ziyarar hadin kai tare da yin Azumi tare da al’ummar Musulmi a fadin duniya.

 Wadannan ayyuka suna tunatar da duniya hakikanin fuskar Musulunci. Kuma ko da yaushe na kan zama mafi samun kwarin gwiwa da kwanciyar hankali a wannan lokaci.

A cikin wannan wata mai alfarma, dukkkanmu muna samun daukaka ta hanyar dabbaka wadannan dabi’u kuma muna rungumar ‘yan uwantaka don gina duniya mai adalci da zaman lafiya ga kowa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Babban Sakataren MDD Ya Taya Musulmi Murnar Shiga Watan Ramadan
  • Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murna Fara Azumin Ramadan
  • Sakon Sakatare Janar Na Majalisar Dinkin Duniya Na Murna Fara Azumin Ramadan
  • Fitaccen Fim Din Na Kasar Sin Mai Suna “Ne Zha 2” Ya Zama Na 7 A Jerin Fina-finai Mafi Samun Kudi A Duniya
  • Rasha Za Ta Bunkasa Kai Wa  Nahiyar Afirka Alkama
  • Jama’ar Duniya Sun Soki Matakin Amurka Na Matsawa Kasashe Ta Hanyar Kakaba Haraji 
  • Shugaban Sin Ya Gana Da Sakataren Majalisar Tsaron Rasha
  • Bude Kasar Sin Na Kyautata Ci Gaban Duniya
  • CMG Ya Kaddamar Da Gasar Basirar Mutum-mutumin Inji Ta Duniya 
  • Taron Sin Da Afrika A Alkahira Ya Bayyana Muhimmancin Kyautata Dangantakar Bangarorin Biyu