Bikin Bazara Na Sinawa Ya Zama Biki Na Al’ummar Duniya
Published: 29th, January 2025 GMT
Bikin bazara shi ne biki mafi dadewa da muhimmanci a bukukuwan gargajiya na Sin. Kuma bikin na ci gaba da kara bazuwa da samun karbuwa a fadin duniya.
A kwanakin baya-bayan nan, kasashe da hukumomin kasa da kasa da dama sun gudanar da shirye-shirye da nune-nunen dake da alaka da bikin bazara, kuma jama’a a fadin duniya sun hadu domin a dama da su cikin bikin murnar sabuwar shekarar ta Sin.
Hakan ba ya rasa nasaba da yadda al’adar ta taba kowanne bangare na rayuwa da kuma sakonnin da take dauke da su kamar na kyautata zumuncin iyali da girmama manya da tausayawa yara, wanda abubuwa ne dake da saukin fahimta ga jama’ar dukkan kasashe. A lokacin guda, ta hanyar bikin bazara, duniya ta ga kasar Sin dunkulalliya mai bude kofa, haka kuma ta shaida nasarorin da kasar ta samu wajen zamanantar da kanta.
Sinawa na mika fatansu na ban kwana da tsohuwar shekara da maraba da sabuwa ga duniya ne ta hanyar bikin bazara. Bikin bazara ba na Sin ba ne kadai, na daukacin duniya ne. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)
কীওয়ার্ড: bikin bazara Bikin bazara
এছাড়াও পড়ুন:
Ba Za A Iya Dakile Ci Gaban Hakkin Dan Adam Na Xizang Da Kowace Irin Karya Ba
A bana aka cika shekaru 60 da kafuwar jihar Xizang mai cin gashin kanta ta kasar Sin. A ranar 28 ga watan Maris, wato ranar tunawa da ’yantar da miliyoyin bayi manoma a Xizang, gwamnatin kasar Sin ta fitar da wata takardar bayani mai taken “Ci gaban hakkin bil’adama a Xizang a sabon zamani”, wadda ta yi amfani da cikakkun bayanai na gaskiya don nuna yadda aka samu manyan sauye-sauye a jihar a cikin shekaru gommai da suka wuce. Takardar ta kuma shaida mana ma’anar “Jin dadin zama ga jama’a babban hakki ne na dan Adam”.
“Ci gaba da aka samu a Xizang ya wuce yadda na yi zato, kuma mutane a nan suna rayuwa irin ta zamani sosai.” Wannan shi ne yadda babban dan jaridar kafar watsa labarai ta 24NewsHD ta kasar Pakistan Ali Abbas ya fada bayan ziyararsa a jihar. A cewarsa, karin mutane a duniya sun fahimci cewa, don neman kawo baraka ga kasar Sin ne wasu kasashen yammacin duniya suke kara wa miya gishiri a batun hakkin bil’adama a Xizang. Sannan game da batun ko an kiyaye hakkin bil’adama da kyau ko a’a a Xizang, bayanan sun riga sun ba da kyakkyawar amsa a kai, kana hakikanan labarun zaman rayuwar jama’ar jihar su ma sun bayyana gaskiya, don haka babu wata karya da za ta iya rufe ko kuma goge ainihin halin da ake ciki a jihar. (Mai fassara: Bilkisu Xin)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp