HausaTv:
2025-04-24@19:21:27 GMT

 Sojojin Sudan Sun Kwance Iko Da Garin “Khartum-al-Bahri”

Published: 29th, January 2025 GMT

A yau Laraba ne dai sojojin Sudan su ka sanar da shimfida ikonsu a garin ‘Khartum-al-Bahri.

Majiyar sojan kasar ta Sudan ta kuma bayyana cewa, a halin yanzu suna aiki tare da bangarorin da suke dace, domin ganin fararen hula mazauna garin sun koma gidajensu a cikin lokaci mafi kusa.

A cikin kwanaki kadan da su ka gabata sojojin na kasar Sudan sun sami nasarar kwace yankuna da dama a kewayen Khartum-al-Bahri da su ka hada da gabashin tekun maliya.

Wannan cigaban da sojojin na Sudan su ka samu, ya biyo bayan korar dakarun rundunar kai daukin gaggawa ne daga babbar shalkwatar soja dake tsakiyar birnin Khartum, haka nan kuma cibiyar sojan ta sadarwa, da babbar cibiyar leken asiri ta soja dake kusa da Khartum-al-Bahri.

 A wata sanawar ta daban da sojojin kasar ta Sudan su ka fitar sun bayyana cewa jiragen yaki sun kai hare-hare a garin al-Fashar da can ne babban birnin yankin Darfur. Wannan yankin shi ne babban sansanin mayakan dakarun rundunar kai daukin gaggawa.

Sojojin na Sudan sun ce, sun kai wadannan hare-haren ne dai da safiyar Yau Laraba.

A wani labarin daga Sudan, rundunar kai daukin gaggawa ta sanar da cewa, an kashe daga cikin kwamandojinta mai suna Rahmatullah al-Mahadi wanda aka fi sani da Jalha a jiya Talata, ba tare da bayyana yadda aka kashe shi din ba.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Khartum al Bahri

এছাড়াও পড়ুন:

Mutanen da aka kashe a Binuwai sun ƙaru zuwa 72

Adadin mutanen da suka mutu a hare-haren da aka kai a Jihar Binuwai ya ƙaru zuwa 72.

Adadin ya ƙaru ne bayan gano ƙarin gawarwaki 13 a ranar Litinin a ƙananan hukumomin  Ukum da Logo.Adadin ya ƙaru ne bayan gano ƙarin gawarwaki 13 a ranar Litinin a ƙananan hukumomin  Ukum da Logo.

Da farko a ranar Lahadi Gwamna Hyacinth Alia a yayin da yake jawabin Ista a wani coci, ya sanar a yayin cewa an gano gawarwaki 59.

Daga bisani aka gano ƙarin gawarwaki a cikin jejin yankunan da aka kai hare-haren.

Kakakin gwmanan jihar, Isaac Uzaan, ya bayyana cewa an gano ƙarin gawarwaki 12 a Ƙaramar Hukumar Uku sauran mutum ɗaya kuma a Logo.

Tsakanin daren ranar Alhamis da safiyar Juma’a ne kai hare-hare a ƙauyukan yankin Sankera wanda ya ƙunshi ƙananan hukumar Ukum, Logo, and Kastina-Ala.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojan HKI Ya Halaka A Gaza
  • Amurka Ta Kai Hare-hare Akan Birane Mabanbanta Na Kasar Yemen
  • ‘Yan Tawayen Sudan Sun Kashe Fararen Hula 47 A Birnin El-Fasher Fadar Mulkin Darfur Ta Arewa
  • An Umurci Sojoji Su Kawarda ‘Yan Bindiga Daga Kwara Da Niger A Cikin Wata Daya
  • Jiragen yakin Amurka sun kara kai hari kan kasar Yemen
  • Ba ‘Yan Nijeriya Ne Ke Kai Mana Hare-hare A Benuwai Ba – Gwamna Alia
  • An sanya dokar hana fita ta sa’o’i 12 a Neja
  • Mutanen da aka kashe a Binuwai sun ƙaru zuwa 72
  • Kungiyar kare farar hula ta Falasdinu ta zargi sojojin da ” kashe-kashe masu yawa”
  • Wang Yi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Sabon Ministan Harkokin Wajen Sudan Ta Kudu