Jaridar “Le Monde” ta kasar Faransa ta dauki labarin da yake cewa iyalai masu yawa sun fice daga HKI baki daya zuwa  kasashen Portugal,Cyprus, da kuma Girka.

Rahoton ya ci gaba da cewa; Dalilan yin hijirar daga HKI zuwa kasashen waje sun kunshi yaki, rashin tsaro da kuma siyasar gwamnatin Benjemine Netanyahu.

Har ila yau, jaridar ta kasar Faransa ta ce, dubban ‘yan share wuri zauna ne suke ficewa daga  Falasdinu dake karkashin mamaya a wasu lokutan iyalai ne kaco kau suke ficewa.

 Kwanaki kadan da su ka gabata wasu iyalai da suke kunshe da mutane 20  da su ka hada iyaye, kakanni da jikoki sun yi hijira zuwa Cyprus domin su rayu a can.

A cikin kafafen sadarwa na al’umma da akwai ‘yan share wuri zauna da dama da suke yin kira da a fice daga HKI zuwa kasashen Girka, Canada da Thailand domin ci gaba da rayuwa a can.

Batun yin hijirar ‘yan sahayoniya daga HKI ya fara ne tun farkon  farmakin Guguwar Aksa, da suke komawa zuwa kasashen turai mabanbanta bayan da su ka tabbatar da cewa, rayuwarsu ba za ta  dawwama ba a cikin kasar da su ka kwace daga masu ita na asali.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: zuwa kasashen

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Da Haddiyar Daular Larabawa Sun Gudanar Da Taron Kwamitin Siyasa Da Al-adu Na Kasashen Biyu

Kasashen Iran da Hadaddiyar Daular Larabawa sun gudanar da taron kwamitin Siyasa da al-adun na kasashen biyu a karon farko a birnin Abu Dhabi wanda ya kara tabbatar da irin ci gaban da suke samu a dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa kyautata dangantaka tsakanin kasashe makobta na daga cikin manufofin JMI ta harkokin wakashen waje.

Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran Majid Takht-e Ravanchi ya bayyana cewa karfafa dangantaka da Hadaddiyar Daular Larabawa yana daga cikin manufofin JMI don biyan bukatun ko wace kasa daga cikin kasashen biyu.

Ya kuma kara da cewa akwai bukatar kasashen musulmi su kara hadin kai a tsakaninsu don magance  matsalar da Falasdinawa suke fuskanta a hannun HKI da kuma kasashen yamma.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasashen Afirka ta Kudu da Malaysia da Colombiya za su hana jiragen ruwa da ke dauke da makamai zuwa Isra’ila
  • Xi Ya Jaddada Ciyar Da Shirin Kasar Sin Mai Kwanciyar Hankali Zuwa Babban Mataki
  • Yadda farashin kayan abinci ya sauka a kasuwannin Arewa
  • Haleyen Kirki 14 Da Ake Bukata Daga Malamin Makaranta (1)
  • Iran Da Haddiyar Daular Larabawa Sun Gudanar Da Taron Kwamitin Siyasa Da Al-adu Na Kasashen Biyu
  • Yawan ’Yan Kasashen Waje Da Suka Shigo Kasar Sin Ba Tare Da Biza Ba A Bara Ya Ninku
  • Kasashen Afrika Ta Kudu, Malasiya Da Colombia Zasu Hana Jiragen Ruwa Dauke Da Makamai Tsayawa A Tashoshin Jiragen Ruwansu
  • Iran Za Ta Rubanya Samar Da Wutar Lantarki Ta Makamashin Nukiliya Har Sau Uku Zuwa 2029
  • Iran Da Saudiyya Sun Tattauna Kan Taron OIC Mai Zuwa
  • Ukraine ta cimma yarjejeniya da Amurka kan haƙar ma’adinai