HausaTv:
2025-03-03@21:26:01 GMT

 Trump Zai Kori Dabilai ‘Yan Kasashen Waje Da Suke Goyon Bayan Hamas Daga Amurka

Published: 29th, January 2025 GMT

Wani jami’in fadar mulkin Amurka ( White Hosue) ya nakalto shugaban kasar Amurka Donald Trump yana fada a yau Laraba cewa, shugaban kasar Amurkan ya rattaba hannu akan wata doka ta fada da kin jinin yahudawa da ta kunshi cewa duk wasu dalibai ‘yan kasashen waje da masu ci rani a kasar,  idan su ka shiga cikin Zanga-zangar nuna goyon bayan Falasdinawa to za a kore su daga Amurka.

Dokar da Trump din yta sanya hannu a kanta ta kuma kunshi bayar da umarni da ma’aikatar shari’ar kasar aka cewa ta bi diddigin duk masu barazanar ta’addanci, da ruruta wutarsa, da mabarnata dake cutar da yahduawan Amurka.”

Haka nan Trump ya ce zai soke izinin shiga cikin kasar ta Amurka da aka bai wa dalibai masu goyon bayan Hamas a cikin dukkanin jami’o’in kasar.

Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya aikewa da dukkanin cibiyoyin kasar ta Amurka umarnin su dauki matakan da su ka dace domin fara korar duk masu fada da Yahudawa, daga ciki har da dabilan jami’oi.

A tsawon lokacin yakin da HKI ta shelanta akan al’ummar Falasdinu, daliban jami’o’in kasar ta Amurka sun rika yin Zanga-zanga da gangami na nuna kin amincewa da halayyar ta Isra’ila, da kuma yin kira ga gwamnatin Amurka da ta kawo karshen sayar da makaman da take yi mata.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Nijar: An Kashe Sojoji 11 A Wani Hari Na Kungiyar al-Ka’ida

Rahotanni da suke fitowa daga Nijar sun bayyana cewa; Wata kungiyar mai alaka da al-ka’ida ta  dauki alhakin kashe sojojin kasar 11 a kan iyaka da Aljeriya.

A ranar Juma’ar da ta gabata ne dai lamarin ya faru,kuma a jiya Asabar ne aka yi jana’izarsu a garin Agadez, kamar yadda wata majiyar watsa labara ta jamhuriyar Nijar ta ambata.

Shafin “Air Info” da ya watsa laabrin ya kuma ce; Jami’an soja da dama sun hjalarci jana’izar sojojin da su ka kwanta dama, daga cikinsu har da janar Musa Salih Barmo, babban hafsan hafsoshin sojan kasar.

Tashar Radiyo din kasar ta Nijar ta ce, an yi wa sojojin kwanton bauna ne a lokacin da suke sintiri akan  mahadar iyakaokin kasar, da Mali da kuma Burkina Faso.

Labarin Radiyon ya kuma ce, Janar Barmo ya nufi asibitin garin Agadez din domin yin dubiyar sojojin da su ka jikkata.”

 A gefe daya wata kungiyar mai  suna; “Nasratul-Islam Wal Muslimin” da reshe ne na alka’ida, ta dauki alhakin kai harin.

A lokuta da dama a baya sojojin na jamhuriyar Nijar sun sha fuskantar hare-hare irin wadannan, sai dai ba kasafai kungiyoyin da suke ikirarin jihadi suke daukar alhakin kai wa ba.

Saharar dake Arewacin Nijar tana da girma kuma tana kusa da kasar Libya da masu hada-hadar mutane da kuma  ‘yan hijira suke bi suna ratsawa domin shiga cikin kasashen turai.

Kungiyar “Ikilid” wacce ba ta gwamnati ba da take sa ido akan duk wasu rikice-rikice da suke faruwa a duniya, ta ce daga 2023 zuwa yanzu an kashe mutane 2400 a cikin wannan kasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda ’yan bindiga suka sace ɗalibai 4 a Jami’ar Tarayya ta Dutsinma
  • Nijar: An Kashe Sojoji 11 A Wani Hari Na Kungiyar al-Ka’ida
  • Shugaban Kasar Ukraine Ya Sami Tarba Mai Kyau A Burtaniya Bayan Cacan Baki Mai Zafi Da Trump
  • Ukraine Da Amurka Sun Kulla Yarjejeniya Kan Ma’adanai – Jami’in Ukraine
  • Zelensky : Ban Ga Laifin Da Na Yi Wa Trump, Ballantana In Nemi Afuwa
  • Al-Houthi : Isra’ila Na fakewa Da Goyan Bayan Amurka Tana Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza
  • Haleyen Kirki 14 Da Ake Bukata Daga Malamin Makaranta (1)
  • A Yau Ce Dokar Haramta Amfani Da Tankunan Mai Masu Daukar Lita 60,000 A Najeriya
  • Iran Da Haddiyar Daular Larabawa Sun Gudanar Da Taron Kwamitin Siyasa Da Al-adu Na Kasashen Biyu
  • An Yi Musayar Yawu A Tsakanin Shugabannin Kasashen Amurka Da Ukiraniya A Fadar White House