Leadership News Hausa:
2025-04-02@16:14:47 GMT

Yankin Gabashin Kongo(Kinshasa) Yana Cikin Yanayi Mai Hadari

Published: 29th, January 2025 GMT

Yankin Gabashin Kongo(Kinshasa) Yana Cikin Yanayi Mai Hadari

Zaunannen wakilin kasar Sin a MDD, Fu Cong, ya bayyana a gun taron gaggawa game da batun Kongo(Kinshasa) da kwamitin sulhu ya kira jiya Talata cewa, a halin yanzu, yankin gabashin Kongo(Kinshasa) yana cikin yanayi mai hadari. Ya ce Sin na goyon bayan mambobin kwamitin sulhu su hada kai tare da daukar kwararan matakai, ta yadda za a samar da dabarun hana yanayin ya ci gaba da tsanani da kuma inganta warware batun a siyasance.

Fu Cong ya bayyana cewa, kwanan nan, yanayin Kongo(Kinshasa) ya shiga matsanancin yanayi ciki sauri, inda kungiyar M23 ta kai hari birnin Goma, hedkwatar jihar Kivu ta arewa dake kasar, lamarin da ya sanya fararen hula da yawa barin gidajensu, inda kuma hadarin barkewar rikici mai girma ke karuwa, wanda ke zaman abun damuwa matuka.

Ya nanata cewa, Sin za ta dage wajen goyon bayan ikon mulkin Kongo(Kinshasa) da mallakar cikakkun yankunanta, kuma tana adawa da dukkanin abubuwan dake keta tsarin dokokin MDD da dokokin kasa da kasa. Haka zalika, bangaren Sin yana bukatar kungiyar M23 ta daina dukkanin ayyukan nuna adawa, kuma ta janye daga yankunan da ta mamaye, kamar Goma.

Fu Cong ya kara da cewa, bangaren Sin yana tir da harin M23 kan ma’aikatan wanzar da zaman lafiya na MDD, kuma yana goyon bayan tawagar MDD dake Kongo(Kinshasa) ta gudanar da ayyukan kare fararen hula, karkashin amincewar kwamitin sulhun. Ya kuma jadadda cewa, babu wata hanyar bude wuta da za ta magance batun gabashin Kongo (Kinshasa), tattaunawa ta diflomasiyya ce kawai mafita. (Safiyah Ma)

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Babu dokar da na karya saboda yin taron a mazaɓata — Natasha

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan da Majalisar Dattawan Nijeriya ta dakatar, ta ce taron barka da sallah da ta yi a mazaɓarta a yammacin Talata duk da haramta taruka da gwamnatin jihar ta yi ba karya doka ba ne.

Ana iya tuna cewa Gwamnatin Kogin dai ta hana duk wani nau’in taro ko gangami a jihar, saboda dalilin da ta ce na tsaro ne.

Haaland zai yi jinyar mako bakwai — Guardiola HOTUNA: Sarki Sanusi ya kai wa Abba ziyarar barka da Sallah

Kwamishinan ‘Yan sandan jihar, Miller Ɗantawaye, ya ce hana taron ya biyo bayan bayanan sirri da suka samu cewa za a samu barzanar tsaro, wanda ya tilasta gwamnatin jihar ɗaukar matakin.

Sai dai Natasha wadda ta isa jihar a wani jirgi mai saukar ungulu, ta bayyana wa magoya bayanta cewa tana da ’yancin kasancewa da mutanenta ta kuma yi shagalin farin ciki tare da su.

“A duk abin da za mu yi, mu sanya Allah a farko kuma mu shigar masa da buƙatunmu ta hanyar addu’a.

“Mijina ya kasance ɗaya daga cikin addu’o’ina da Allah Ya amsa. In banda haka ta yaya ni da ba kowa ba ce fa ce talaka daga ƙabilar Ebira na samu ƙarfin samun jirgin da zai kawo ni gida?

“Goyon bayan mijina ne ya kawo haka, kuma shi ke ciyar da ni gaba a koda yaushe.

“Tun jiya da na samu labarin za a rufe hanyoyi, aka kuma haramta taruka da jerin gwanon motoci a cikin gari na san cewa mu ne ake so a muzgunawa.

“Amma sai na faɗa wa kaina ai ba kakar siyasa ko yaƙin neman zaɓe ba ne yanzu.

“Don haka ni ba yaƙin neman zaɓe zan yi ba. Ni kaɗai ce zan shigo gari cikin mutane na, na yi shagalin bikin Sallah tare da su.

“Don haka babu wani laifi a ciki, babu dokar da na karya. A Najeriya muke. Ina da ’yancin shiga taruka da bukukuwa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Za Ta Yi Ramuwar Gayya Kan Takunkumin Biza Da Amurka Ta Kakaba Wa Jami’anta
  • Babu dokar da na karya saboda yin taro a mazaɓata — Natasha
  • Babu dokar da na karya saboda yin taron a mazaɓata — Natasha
  • HKI Ta Sake Kai Wa Unguwar Dhajiya Dake Beirut Hari
  • Mene ne matsayin azumin Sitta Shawwal a Mazhabar Malikiyya
  • Nijar Ta Fice Daga Rundunar Tsaro Ta Haɗin Kai MNJTF
  • Gwamnan Edo Ya Ziyarci Sanata Barau Kan Kisan Yan Arewa 16
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci: Kasashen Yamma Sune Yan Ta’adda Na Gasliya A Yankin
  • Dan shekara 4 ya kira wa mahaifiyarsa ’yan sanda
  • Iran: Amurka ta hada kai da Isra’ila wajen kawo cikas ga harkar tsaro a gabas ta tsakiya