Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-04-02@15:35:54 GMT

Maniyatan Jihar Kaduna Na Bana Sun Fara Karbar Horo

Published: 29th, January 2025 GMT

Maniyatan Jihar Kaduna Na Bana Sun Fara Karbar Horo

Hukumar Alhazan Jihar Kaduna ta Kaddamar da shirin bada horo da fadakarwa ga maniyatan bana

Jami’in hulda da jama’a na hukumar Yunusa Muhammad Abdullahi ya bayyana cewa an gabatar da wannan bitar ko horon ne a cibiyar hukumar alhazai ta jihar Kaduna da ke unguwar Dogarawa a karamar Hukumar Sabon Garin Zaria.

Shugaban hukumar na jihar Kaduna Malam Salihu Abubakar yace bitar wani jigo ne ga kokarin da ake wajen ilmantar da maniyata yadda zasu sauke farali salun alun.

Za a fadakar da maniyatan game dukkanin abubuwan da suka shafi aikin hajji domin fuskantar kowane irin kalubalen da zai taso lokacin aikin hajji mai zuwa.

Malam Abubakar ya roki mabiyatan su kammala biyan kudin aikin bana kafin cikar wa’adin da hukumar aikin hajji ta kasa ya cika wacce ta warewa jihar Kaduna maniyata dubu 6.

A jawabinsa, shugaban sashen gudanarwa na hukumar aikin hajji ta jihar Kaduna Alhaji Abubakar Usman Yusuf yayi bayanin cewa za a ci gaba da bada wannan horon a kowane karshen mako a dukkanin kananan hukumomin jahar 23.

Shi kuma.shuganan karamar hukumar Sabon Garin Zaria Malam Jamilu Abubakar Albani wanda ya samu wakilcin mataimakin sa Alhaji Abdulkareem Kamalu ya jaddada bukatar maniyata su kiyaye dokokin kasar Saudiyya dama na Nijeriya a lokacin aikin hajjin bana.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: jihar Kaduna

এছাড়াও পড়ুন:

HOTUNA: Sarki Sanusi ya kai wa Abba ziyarar barka da Sallah

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya karɓi baƙuncin Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, a fadar gwamnatin jihar.

Sarkin dai ya kai wa gwamnan ziyarar ce kamar yadda aka saba a Hawan Nassarawa da ake gudanarwa bisa al’ada duk shekara.

Gangamin da zan yi a mazaɓata babu fashi — Natasha Muna kiran Natasha ta jingine gangamin da za ta yi a Kogi — ’Yan sanda

Sai dai a sakamakon haramcin gudanar da haye-hayen sallah da rundunar ’yan sandan jihar ta yi, Sarkin bai cika duk tsare-tsaren da al’ada ta tanada ba na gudanar da Hawan Sallah.

Aminiya ta ruwaito cewa, Sarkin wanda ya yi ƙoƙarin kawar da idon jama’a, ya bi ta wasu hanyoyin da ba su aka saba bi wajen kai wa gwamna ziyara a yayin gudanar da hawa cikakke.

Haka kuma, Sarkin ya yi amfani da jerin gwanon motoci ƙalilan maimaiko hawa dawakai

Sai dai an tsananta tsaro a duk hanyoyin da Sarkin ya bi tun daga Fadar Sarki ta Gidan Ƙofar har zuwa Gidan Gwamnatin Kano.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Basakkwacen da ya yi ridda ya sake karɓar addinin Musulunci
  • Iran Ta Bukaci Hukumar IAEA Ta Bayyana Matsayinta A Shirin Makamashin Nukliya Na Kasar
  • Duk Da Hanin Gwamna Da ‘Yansanda, Natasha Ta Isa Gida Kuma Ta Yi Taro
  • HOTUNA: Sarki Sanusi ya kai wa Abba ziyarar barka da Sallah
  • Muna kiran Natasha ta jingine gangamin da za ta yi a Kogi — ’Yan sanda
  • Tawagar Aikin Ceto Ta Kasa Da Kasa Ta Kasar Sin Ta Isa Myanmar
  • Sani Ahmad Lere Na Radio Nijeriya Kaduna Ya Zama Falakin Lere
  • Gwamnan Edo Ya Ziyarci Sanata Barau Kan Kisan Yan Arewa 16
  • Tsawa Ta Kashe Makiyayi Da Shanu A Kudancin Kaduna
  • Sarkin Gombe ya nemi manoma da makiyaya su zauna lafiya