Maniyatan Jihar Kaduna Na Bana Sun Fara Karbar Horo
Published: 29th, January 2025 GMT
Hukumar Alhazan Jihar Kaduna ta Kaddamar da shirin bada horo da fadakarwa ga maniyatan bana
Jami’in hulda da jama’a na hukumar Yunusa Muhammad Abdullahi ya bayyana cewa an gabatar da wannan bitar ko horon ne a cibiyar hukumar alhazai ta jihar Kaduna da ke unguwar Dogarawa a karamar Hukumar Sabon Garin Zaria.
Shugaban hukumar na jihar Kaduna Malam Salihu Abubakar yace bitar wani jigo ne ga kokarin da ake wajen ilmantar da maniyata yadda zasu sauke farali salun alun.
Za a fadakar da maniyatan game dukkanin abubuwan da suka shafi aikin hajji domin fuskantar kowane irin kalubalen da zai taso lokacin aikin hajji mai zuwa.
Malam Abubakar ya roki mabiyatan su kammala biyan kudin aikin bana kafin cikar wa’adin da hukumar aikin hajji ta kasa ya cika wacce ta warewa jihar Kaduna maniyata dubu 6.
A jawabinsa, shugaban sashen gudanarwa na hukumar aikin hajji ta jihar Kaduna Alhaji Abubakar Usman Yusuf yayi bayanin cewa za a ci gaba da bada wannan horon a kowane karshen mako a dukkanin kananan hukumomin jahar 23.
Shi kuma.shuganan karamar hukumar Sabon Garin Zaria Malam Jamilu Abubakar Albani wanda ya samu wakilcin mataimakin sa Alhaji Abdulkareem Kamalu ya jaddada bukatar maniyata su kiyaye dokokin kasar Saudiyya dama na Nijeriya a lokacin aikin hajjin bana.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: jihar Kaduna
এছাড়াও পড়ুন:
Hisba ta kama wasu matasa ba sa azumi a Kano
Hukumar Hisba ta Jihar Kano, ta kama wasu matasa da ba su yi azumi a ranar farko ta watan Ramadan ba.
Mataimakin Kwamanda Janar na Hukumar, Dokta Mujahideen Abubakar ne, ya tabbatar da kama matasan.
Sojoji sun ƙwato makamai a dajin Sambisa Miji ya kashe matarsa saboda abincin buɗa-baki a BauchiHakazalika, ya tabbatar da cewa jami’an Hisba sun cafke su yayin sintiri da suka yi a sassa daban-daban na Kano.
Har ila yau, hukumar ta kama wasu matasa ku san 60 bisa laifin askin banza, wanda ta ce ya saɓa wa dokokin addini da al’ada.
Bugu da ƙari, an kama wasu direbobin Adaidaita Sahu da ake zargi da cakuɗa maza da mata a cikin abin hawa, abin da hukumar ta ce ba za ta yarda da shi ba.
Hisba ta ce za ta ci gaba da sintiri domin tabbatar da an kiyaye dokokin Shari’a a lokacin watan Ramadan.