Aminiya:
2025-04-22@07:08:42 GMT

Mutum 20 sun rasu a hatsarin jirgin sama a Sudan ta Kudu

Published: 29th, January 2025 GMT

Aƙalla mutane 20 ne ska rasu a wani hatsarin jirgin sama da ya auku a Jihar Unity da ke Sudan ta Kudu.

Rahoton gidan rediyon Miraya, na tawagar Majalisar Ɗinkin Duniya da ke ƙasar, ya bayyana cewa jirgin ya yi hatsari ne jim kaɗan bayan tashinsa daga wata rijiyar mai a Unity, inda ya ɗauki hanyarsa ta zuwa babban birnin ƙasar, Juba.

An dakatar da Max Air na tsawon wata 3 bayan hatsari a Kano Jami’an tsaro sun mamaye sakatariyar PDP bayan ɓarkewar rikici

Jirgin yana ɗauke da fasinjoji 21 da kuma ma’aikatan jirgin lokacin da hatsarin ya auku.

Rahotanni sun tabbatar da cewa matuƙin jirgin ya rasu, yayin da mutum ɗaya kacal ya tsira da ransa, sai dai yana cikin mawuyacin hali.

A baya-bayan nan, hatsarin jiragen sama ya ƙaru a Sudan ta Kudu, musamman sakamakon rashin isassun kayan fasaha da kuma matsalolin tsaro a filayen jiragen sama.

A shekarar 2018, wani jirgin sama mai ɗauke da fasinjoji 19 ya faɗi a yankin Yirol, inda mutum 17 suka rasu.

Gwamnatin Sudan ta Kudu, ta sha alwashin yin bincike kan wannan hatsari da kuma ɗaukar matakan da suka dace don rage irin waɗannan haɗura a nan gaba.

A halin yanzu, hukumomi na ci gaba da bincike domin gano musabbabin aukuwar wannan hatsari.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

An Fara Bikin Ranar Sojin A Iran 18 Ga Watan Afrilu Tare Da Gudanar da Fareti A Gaban Shugaban Kasar

An fara gudanar da bukukuwan ranar soji a Iran a ranar 18 ga watan Afrilu ta hanyar gudanar da faretin soja a gaban shugaban kasar Mas’ud Pezeshkian

An fara faretin soji na sojojin kasar Iran a kusa da hubbaren Imam Khumaini (r.a) da ke kudancin birnin Tehran fadar mulkin kasar a daidai lokacin da ake gudanar da bukukuwan ranar sojoji ta 18 ga watan Afrilu.

A jiya Juma’a 18 ga watan Afrilu ne sojojin kasar Iran suka fara faretin soji na murnar zagayowar ranarsu da kuma irin bajintar jarumtakar sojojin kasar, a kusa da hubbaren Imam Khumaini (r.a) da ke kudancin  babban birnin kasar Tehran.

A cewar kamfanin dillancin labaran IRNA na Iran, faretin ya samu halartar shugaban kasar Mas’ud Pezeshkian da manyan kwamandojin sojojin kasar Iran.

Faretin dai zai kunshi rundunonin yaki da motoci masu sulke na rundunar sojojin kasa na kasar, mayakan sojin sama, makamai da na’urorin tsaro na sojojin sama, da na’urorin sojan ruwa da ake iya jigila da su.

Haka kuma za a baje kolin wasu daga cikin nasarorin da Iran ta samu, da makamai masu linzami, na sama, da na ruwa, da kuma na kasa gami da jiragen sama marasa matuka ciki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wang Yi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Sabon Ministan Harkokin Wajen Sudan Ta Kudu
  • Bikin Ista: Hatsarin mota ya laƙume rayuka 5 a Gombe
  • Fafaroma Frasncis ya rasu yana da shekaru 88
  • Paparoma Frasncis ya rasu yana da shekaru 88
  • Fafaroma Francis ya Rasu
  • Gobara ta ƙone gidaje sama da 100 a sansanin ’yan gudun hijira a Borno 
  • Leicester City Ta Koma Gasar Yan Dagaji Bayan Shan Kashi A Hannun Liverpool
  • Sharhi:  Kalankuwar  Kona Rayayyu Da Wuta A Gaza
  • Muna Ganin Kashe-kashe Ta Ko’ina – ‘Yan Gudun Hijirar Sudan
  • An Fara Bikin Ranar Sojin A Iran 18 Ga Watan Afrilu Tare Da Gudanar da Fareti A Gaban Shugaban Kasar