Aminiya:
2025-03-02@21:47:32 GMT

Mutum 20 sun rasu a hatsarin jirgin sama a Sudan ta Kudu

Published: 29th, January 2025 GMT

Aƙalla mutane 20 ne ska rasu a wani hatsarin jirgin sama da ya auku a Jihar Unity da ke Sudan ta Kudu.

Rahoton gidan rediyon Miraya, na tawagar Majalisar Ɗinkin Duniya da ke ƙasar, ya bayyana cewa jirgin ya yi hatsari ne jim kaɗan bayan tashinsa daga wata rijiyar mai a Unity, inda ya ɗauki hanyarsa ta zuwa babban birnin ƙasar, Juba.

An dakatar da Max Air na tsawon wata 3 bayan hatsari a Kano Jami’an tsaro sun mamaye sakatariyar PDP bayan ɓarkewar rikici

Jirgin yana ɗauke da fasinjoji 21 da kuma ma’aikatan jirgin lokacin da hatsarin ya auku.

Rahotanni sun tabbatar da cewa matuƙin jirgin ya rasu, yayin da mutum ɗaya kacal ya tsira da ransa, sai dai yana cikin mawuyacin hali.

A baya-bayan nan, hatsarin jiragen sama ya ƙaru a Sudan ta Kudu, musamman sakamakon rashin isassun kayan fasaha da kuma matsalolin tsaro a filayen jiragen sama.

A shekarar 2018, wani jirgin sama mai ɗauke da fasinjoji 19 ya faɗi a yankin Yirol, inda mutum 17 suka rasu.

Gwamnatin Sudan ta Kudu, ta sha alwashin yin bincike kan wannan hatsari da kuma ɗaukar matakan da suka dace don rage irin waɗannan haɗura a nan gaba.

A halin yanzu, hukumomi na ci gaba da bincike domin gano musabbabin aukuwar wannan hatsari.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Yan Ta’adda Sun kashe Sojojin Sa Kai Na Basij Biyu A Yankin Kudu Maso Gabacin Kasar Iran

Rundunar Basij a yankin kudu maso gabacin kasar Iran ta bada sanarwan shahadar dakarunta guda biyu a jiya Asabar.

Kamfanin dillancin labaran tasnim na kasar Iran, ya nakalto rundunar IRGC na yankin ya na bada sanarwan shahadar Hojjatoleslam Sadeq Mahmoudi da kuma Milad Damankesh a lokacinda suke komawa gida daga wurin aiki a cikin wata mota tasu.

Labarin ya kara da cewa shahidan biyu sun hadu da ajalinsu ne a lokacinda wasu yan ta’adda suka bude wuta a kan motarsu a lokacinda suke wucewa a wata unguwa zuwa gidajensu.

Lardin Sitan Baluchistan wanda ke kan iyaka da kasar Pakistan dai ya dade yana fada da kungiyoyin yan ta’adda wadanda suke shigowa kasar daga kasar Pakistan, wadanda kuma suke samun taimako kasashe waje, musamman kasashen yamma da wasu kasashe makobta.

Wata kungiya wacce ake kira ‘Jashul Adle” ce ta saba daukar nauyin kashe mutane a yankin, fararen hula da sojoji wadanda suke taimakawa don tabbatar da zaman lafiya a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga sun hallaka mutum 6 a ƙauyukan Kebbi
  • ’Yan bindiga sun hallaka mutum 6 ƙauyukan Kebbi
  • Masar ta ki amincewa da duk wani yunkuri na kafa gwamnatin ‘yan adawa a Sudan
  • Mahara sun yi basaja da kayan EFCC wajen sace mutum 10 a otal
  • Fasinjoji 12 sun ƙone ƙurmus a hatsarin mota a Edo
  • Kasashen Somaliya Da Habasha Suna Gab Da Rattaba Hannu Akan Amfani Da Tashar Jirgin Ruwa
  • Yan Ta’adda Sun kashe Sojojin Sa Kai Na Basij Biyu A Yankin Kudu Maso Gabacin Kasar Iran
  • Sarkin Sasa ya rasu bayan shafe shekaru 125 a doron ƙasa
  • Gobara ta hallaka mutum 2 a sansanin ’yan gudun hijira a Borno
  • Kasashen Afrika Ta Kudu, Malasiya Da Colombia Zasu Hana Jiragen Ruwa Dauke Da Makamai Tsayawa A Tashoshin Jiragen Ruwansu