Fannonin Da Xi Jinping Ya Lura Da Su A Ziyararsa A Arewa Maso Gabashin Sin
Published: 29th, January 2025 GMT
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kan yi rangadi a wurare daban daban kafin bikin bazara na kasar, kana kafin bikin na wannan shekara, shugaban ya ziyarci lardin Liaoning dake arewa maso gabashin Sin. Sai dai wadanne fannonin ya mai da hankali a kai, yayin wannan ziyara?
Abu na farko da shugaba Xi ya lura da shi, shi ne aikin sabunta fasahohin masana’antu.
Sa’an nan abu na biyu da shugaba Xi Jinping ya sa lura a kai shi ne yadda ake kula da jama’ar da bala’in ambaliyar ruwa ya ritsa da su a bara. Yayin da fanni na uku shi ne yadda kasuwannin wurin suke samar da isasshen kayayyakin abinci masu inganci ga jama’a, a lokacin bikin bazara na gargajiya.
Cikin wata unguwa, shugaba Xi ya ce, wani abu mafi faranta rai shi ne ganin yadda jama’a suke jin dadin rayuwa. Ya ce ya kamata a kara kokarin tabbatar da haka a ko da yaushe. (Bello Wang)
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Komawa Cin Abinci Yadda Ya Kamata Bayan Watan Ramadana
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Watan azumin Ramadana kan zo da sauye sauye da dama da suka haɗa da ƙara ƙaimi wajen bauta wa ubangiji, samun lada ta hanyar ciyar da al’umma da kuma falala masu yawa da ba su misaltuwa.
Wani sauyi da watan azumin watan Ramadana ke zuwa da shi shi ne canjin yanayin cimar al’umma, inda mutane ke canzawa daga cin abinci sau uku ko sama da haka a rana zuwa sahur da kuma buɗe-baki.
Bayan kwanaki 29 zuwa talatin na samun waɗannan canji, ta waɗanne hanyoyi ne al’umma za su koma cimaka kamar yadda suka saba gabanin watan Ramadana
NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Ya Kamata Musulmi Su Yi Kafin Da Kuma Ranar Sallah DAGA LARABA: Yadda Farashin Kayan Masarufi Suke Gabanin SallahShirin Najeriya A Yau zai yi nazari ne kan hanyoyin da mutum ya kamata ya bi don komawa cin abinci yadda ya kamata bayan azumtar watan Ramadana.
Domin sauke shirin, latsa nan