Aminiya:
2025-04-08@07:52:02 GMT

EFCC ta cafke tsohon shugaban NHIS, Usman Yusuf a Abuja

Published: 30th, January 2025 GMT

Jami’an Hukumar Yaƙi da Yi Wa Tattalin Arziƙi Zagon Ƙasa (EFCC), sun cafke Tsohon Shugaban Hukumar Inshorar Lafiya ta Ƙasa (NHIS), Farfesa Usman Yusuf, bayan kai sumame a gidansa da ke Abuja.

Aminiya ta tabbatar da cewa jami’an EFCC ɗauke da makamai sun isa gidansa da misalin ƙarfe 4:46 na yammacin ranar Laraba, inda suka kama shi a gaban matarsa da ’ya’yansa.

Mutum 20 sun rasu a hatsarin jirgin sama a Sudan ta Kudu Jami’an tsaro sun mamaye sakatariyar PDP bayan ɓarkewar rikici

Sai dai har yanzu ba su bayyana dalilin cafke shi ba.

Wata majiya ta bayyana cewa an kama tare da tafiya da Farfesa Yusuf zuwa wani waje da ba a bayyana ba.

Duk da cewa hukumomi ba su fitar da sanarwa kan tuhumar da ake yi masa ba, wasu majiyoyi sun ce kamun nasa yana da alaƙa da shugabancin da ya yi a hukumar NHIS.

Wani babban jami’in EFCC ya ce, “Ba za a iya bayyana dalilin kama shi a yanzu ba saboda har yanzu ana bincike.

“Amma yana hannunmu kuma zai taimaka wajen gudanar da bincike.”

An cire Yusuf daga muƙaminsa a shekarar 2019 a lokacin mulkin tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari.

Wani kwamitin bincike na Ma’aikatar Lafiya ne, ya bayar da shawarar korarsa bisa zargin ɓatan-dabon Naira miliyan 919.

Da aka tuntuɓi kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya ce zai bincika batun sannan ya yi ƙarin haske daga baya.

Sai dai har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, bai yi martani ba.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Kananan Cibiyoyin Kiwon Lafiya 8,880 A Duka Fadin Kasar

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta bada sanarwan cewa ta ware kudade don gina kananan cibiyoyin kiwon lafiya a duk fadin kasar.

Jaridar daily Trust ta Najeriya ta nakalto mataimakin shugaban kasa Alhaji Shetima yana fadar haka a ranar Asabar a lokacinda yake kaddamar da cibiyar yaki da cutar daga a cikin asbitin koyon aikin likitanci ta OOUTH dage birnin shagamu na jihar Oyo.

Mataimakin shugaban kasar ya kara da cewa shirin gina wadannan kananan cibiyoyin kiwon lafiya dai yana daga cikin babban shirin gwamnatin mai ci na kyautata cibiyoyin kiwon lafiya a kasar gaba daya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Saudiyya ta musanta hana ’yan Nijeriya biza
  • ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zanga A Karkashin Jagorancin Sowore A Abuja
  • Shugaban Hukumar IAEA Ya Ce JMI Bata Da Makaman Nukliya
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Kananan Cibiyoyin Kiwon Lafiya 8,880 A Duka Fadin Kasar
  • Tsohon Gwamnan Oyo, Omololu Olunloyo, Ya Rasu Yana Da Shekaru 89
  • Burtaniya Ta Soki Gwamnatin Netanyahu Kan Hana ‘Yan Majalisarta Biyu Shiga Cikin Isra’ila
  • Tsohon Gwamnan Oyo Olunloyo ya riga mu gidan gaskiya
  • Guteress : ba wadan zai ci ribar yakin cinikayya
  • Red Crescent ta Falasdinu ta nemi a yi bincike kan kisan da Isra’ila ta yi wa ma’aikatan agaji
  • Koch Usman Abdullahi Zai Jagoranci Kano Pillars A Karon Farko Bayan Dakatarwa