Yayin da dokar haramtawa hukumar kula da ‘yan gudun hijirar Palasdinu ta MDD (UNRWA) yin aiki a Isra’ila ke gab da fara aiki, kwamitin sulhu na majalisar ya kira wata budaddiyar muhawara dongane da batun, inda wakilin Sin da wakilan sauran kasashe suka sake bayyana goyon bayansu ga hukumar.

Wakilin Sin na dindindin a MDD Fu Cong, ya yi kira ga Isra’ila da ta daina dakatarwa da kai wa hukumar hari, kana ta dakatar da zartar da dokoki masu ruwa da tsaki, yana mai kira ga kasashen duniya su ci gaba da goyon bayan hukumar wajen gudanar da ayyukanta da marawa MDD da kwamitin sulhun baya, wajen daukar matakan gaggawa domin tabbatar da hukumar ta gudanar da ayyukanta.

Yankin Gabashin Kongo(Kinshasa) Yana Cikin Yanayi Mai Hadari “the pen writes the dragon and snake”(shirin da ya nuna fasahar rubutu na Sinanci da wasan Kunfu)

A cewar Fu Cong, goyon bayan hukumar na da alaka da kiyaye ikon tsarin dokokin kasa da kasa da kuma huldar kasashe da bangarori daban-daban da kiyaye rayukan miliyoyin ‘yan Gaza da kwanciyar hankalin yankin yamma da kogin Jordan da kuma warware batun Palasdinu a siyasance.

Fu cong ya kuma nanata cewa MDD da kwamitin sulhu na da nauyin daukar matakai na gagagwa da suka dace, domin tabbatar da hukumar na gudanar da ayyukanta da kuma kare yunkurin kakaba matakin ladaftarwa na bai daya kan al’ummar Gaza. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ruftawar gini ta kashe mutum 5 a Legas

Kawo yanzu an samu aƙalla mutum biyar da suka riga mu gidan gaskiya a sanadiyyar ruftawar wani bene mai bene mai hawa uku da ya ruguje a unguwar Ojodu-Berger da ke Jihar Legas.

Haɗarin ya faru ne da misalin ƙarfe 09.45 na safiyar ranar, inda hukumar kai ɗauki gaggawa tare da taimakon ’yan sanda suka gano cewa wani gini mai hawa uku ɗauke da gidan abinci da mashaya ne ya ruguje.

Mayaƙan ISWAP sun tarwatsa gada a Yobe Kada Kanawa su bari rigingimun siyasa su hana su zaman lafiya — Shettima

Jami’in hukumar bayar da agajin, Ibrahim Farinloye, ya ce daga faruwar lamarin zuwa yanzu an ceto mutane 20 jimilla da suka maƙale a ƙarƙashin baraguzai.

“Sai dai abin takaicin shi ne cikin gawawwakin mamatan biyar da aka samu akwai mata uku da maza biyu.”

Shi ma da yake nasa jawabin a ranar Lahadi, babban Sakataren hukumar LASEMA, Olufemo Oke-Osanyintolu, ya ce mamatan biyar da aka samu an killace su a ɗakin ajiyar gawawwaki na asibiti.

Da farko dai babu labarin mutuwa, sai dai an samu asarar dukiya, amma yanzu bayan ci gaba da aikin ceto, an gano gawawwaki a cikin waɗanda suka maƙale a ƙarƙashin baraguzai.

’Yan sanda da hukumar kai dauƙin gaggawa sun ci gaba da bincike domin gano musabbabin rugujewar ginin.

Jami’ai na hukumar LASEMA na ci gaba da binciken baraguzan ginin da nufin gano ko da sauran mutane a ciki.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin: Amurka Ta Buga Harajin Fito Kan Sassa Daban Daban Ba Tare Da Nuna Sanin Ya Kamata Ba
  • Iran Zata Gudanar Da Tarin Kare Hakkin Bil’adama Ta Faskar Gabacin Duniya A Karo Na Farko
  • Nda-Isaiah Ta Yaba Wa Matar Shugaban Kasa Tinubu Kan Soyayya Da Tallafawa Talakawan Nijeriya
  • Iran Ba Ta Da Niyyar Tattaunawa Da Amurka A Fili Bainar Jama’a Kan Shirinta Na Makamashin Nukiliya
  • Kungiyar Hamas Ta Bukaci Goyon Baya Daga Sauran Falasdinawa Na Gabar Yammacin Kogin Jordan
  • Kakakin Ma’aikatar Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Babban Abin Da Suke Bukata Shi Ne Daga Takunkumi
  • Bikin Easter : Paparoma Francis ya yi kira da a tsagaita wuta a Gaza
  • Jakadan Sin A Amurka: Beijing Na Adawa Da Duk Wani Nau’in Karin Haraji Ko Yakin Ciniki
  • Ruftawar gini ta kashe mutum 5 a Legas
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Yaba Da Zaman Tattaunawan Iran Da Amurka Zagaye Na Biyu A Birnin Roma