Aminiya:
2025-03-03@09:15:52 GMT

NAJERIYA A YAU: Ainihin Dalilan Taƙaddama Kan Kafa Kotunan Musulunci A Kudu

Published: 30th, January 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Ana ci gaba da zazzafar muhawara a shiyyar Kudu maso Yammacin Najeriya a kan batun samar da kotunan Shari’ar Musulunci.

Majalisar Ƙoli ta Harkokin Addinin Musulunci a yankin ce dai ta buƙaci hakan. Sai dai wasu ƙungiyoyi da ma ɗaiɗaikun mutane a yankin suna adawa da wannan buƙata.

NAJERIYA A YAU: Dabarun Noma Don Samun Kuɗaɗen Shiga DAGA LARABA: Dalilan Da Mutane Suke Son Haihuwar Maza Fiye Da Mata

Wannan ne batun da shirin Najeriya a Yau na wannan lokacin zai yi nazari a kai.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Masar Za Ta Bayyana Shirin Sake Gina Gaza A Yayin Taron Larabawa

Babban jami’in diplomasiyyar kasar Masar ya sanar da cewa; Shirin da kasarsa take da shi na sake gina Gaza, abu ne mai yiyuwa a aikace, kuma za a aiwatar da shi ba tare da an kori mutane su bar Gaza ba.

Badr Abdul’adhy,  ya bayyana hakan ne a yayin ganawa da fira ministan gwmanatin kwarya-kwaryar Falasdinu gabanin yin taron kasashen larabawa a birnin alkahira.

Ministan harkokin wajen kasar ta Masar ya ce; “Hanya daya tilo ta kawo karshen yawan fadace-fadace, shi ne a  cusa wa Falasdinawa fatan jin cewa,abinda suke mafarki da shi mai yiyuwa ne a aikace,wanda shi ne kafa ‘yantacciyar kasarsu.”

Haka nan kuma ya ce; Shirin da Masar take da shi na sake gina Gaza, mai yiyuwa ne a aikace, kuma cikin wani matsakaicin zango na lokaci, bai kuma bukatar a ce sai mutane sun bar kasarsu.”

 Wannan shirin na Masar dai ya zo ne bayan da shugaban kasar Amurka Donald Trump ya  ce za a kori Falasdinawa su miliyan biyu daga Gaza saboda sake ginata da kuma yin wasu manyan gine-gine na kasuwanci.

Kalaman na shugaban kasar Amurka sun fuskanci mayar da martani mai tsanani daga Falasdinawa, kasashen Larabawa, da kuma  wasu kasashen turai.

A nashi gefen, Fira ministan Falasdinu Muhammad Mustafa ya bayyana fatansa na samun cikakken goyon bayan kasashen larabawa domin aiwatar da shirin na kasar Masar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Lavrov Ya Yi Watsi Da Batun Aike Wa Da Dakarun Zaman Lafiya A Kasar Ukiraniya
  • Masar Za Ta Bayyana Shirin Sake Gina Gaza A Yayin Taron Larabawa
  • NAJERIYA A YAU: Yadda za ku yi girke-girken azumi da kuɗi kaɗan
  • Masar ta ki amincewa da duk wani yunkuri na kafa gwamnatin ‘yan adawa a Sudan
  • Yan Ta’adda Sun kashe Sojojin Sa Kai Na Basij Biyu A Yankin Kudu Maso Gabacin Kasar Iran
  • A Yau Ce Dokar Haramta Amfani Da Tankunan Mai Masu Daukar Lita 60,000 A Najeriya
  • An ga watan Ramadan a Najeriya — Sarkin Musulmi
  • An ga watan Ramadan a Najeriya —Sarkin Musulmi
  • Shirin Zamanantar Da Aikin Noma Na Sin Na Samar Da Damar Bunkasa Bangaren A Afirka 
  • Cibiyar bincike ta nemi a tabbatar da dokar kare haƙƙin mata a Arewa