Shugaban kasar Amurka ya rattaba hannu kan dokar ba da damar tsare bakin haure kusan 30,000 a sansanin Amurka da ke tsibirin Guantanamo

Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya ce yana son gidan kurkukun sojoji da ke Guantanamo Bay, wanda aka kebance domin tsare fursunonin da ake zargi da ta’addanci, ya kasance a shirye domin karban bakin haure kusan 30,000 da suka shiga cikin Amurka ba bisa ka’ida ba.

Trump yana cewa: “A yau zai rattaba hannu kan wani umarni na zartarwa wanda ke umurtar ma’aikatar tsaro da tsaron cikin gida da su shirya wata cibiya da za ta karbi bakin haure 30,000 a tsibirin Guantanamo Bay,” Trump ya kara da cewa: Guantanamo zai karbi “masu aikata laifuka” a cikin wani yanayi na yau da kullun ba na sojojin yaki ba.

Shugaban na Amurka ya kuma rattaba hannu kan dokarsa ta farko tun bayan hawansa mulki a ranar 20 ga watan Janairu, wani mataki na nuna adawa da shige da fice wanda ke ba da damar tsare mutane kai tsaye a cikin wani yanayi da ba na soji ba idan aka tuhume su ko kuma aka yi musu shari’a a kan aikata wasu laifuffuka ko keta hurumin wasu dokoki.

An bude gidan yarin na Guantanamo ne a shekara ta 2002, a cikin wani sansanin sojin Amurka da ke Cuba, a matsayin wani bangare na yaki da ta’addanci da tsohon shugaban Amurka George W. Bush ya ayyana bayan kai harin ranar 11 ga watan Satumban shekara ta 2001.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sharhin Bayan labarai: Rage Kasafin Kudin Ma’ailatar harkokin wajen Amurka da tasirinsa

Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka, sharhin bayan labarammu na yau za yi magana dangane da “Rage kisasfin kudan ma’aikatar harkokin wajen Amurla da kimani kasha 50% da kuma tasirinsa ga matsayin Amurka a duniya da kuma cikin gida. Wanda ni tahir amin zan karanta.

A makon da ya gabata ne shugaban kasar Amurka Donal Trump ya bada sanarwan, rahe kasafin kudi na ma’aikatar harkokin wajen kasar da kasha 50%, saboda haka kuma ya rufe wasu daga cikin ofisoshin jakadancin kasar da kananan ofisoshin jakadancin kasar fiye da 30 a yankuna daban daban a duniya amma mafi yawansu a nahiyar Afirka.

Dangane da wannan matakin da gwamnatin kasar Amurka masana daga ciki ga wajen kasar ta Amurka masu yawa sun nuna damuwarsu da kuma rashin amincewarsu da hakan.

A majalisar dokokin kasar, wakilai daga jam’iyyu biyu masu mulkin Amurka wato Republican da kuma Democrat sun nuna rashin amincewarsu da matakan da shugaba Trump ya dauka, suna kuma ganin hakan wata alama ce jada bayan Amurka daga harkokin kasashen duniya, kuma da haka tauraron kasar zata dushe a duniya. Sannan akwai has ashen cewa kasar China zata maye gurbin Amurka a cikin al-amura da dama, musamman a kasashen da Amurka ta janye.

Kafin haka dai shugaban kasar Amurka ya janye kasar Amurka daga manya-manayn kungiyoyin bada agaji a duniya, wadanda suka hada da hukumar lafiya ta duniya WHO, hukumar abinci ta duniya.

Banda haka Amurka ta janye tallafin da take bawa kungiyar tsaro ta NATO wanda yake taimakawa abokan kasar na turai kan abubuwan da suka shafi tsaro, da kuma wasu al-amur da dama.

Masu sukan shugaban daga cikin har da sanatoci da tsoffin janar-janar na sojojin Amurla wadanda suka yi ritaya kimani 120 suke ganin, shugaban trump ya mikawa kasashen China da rasha dukkan wuraren da ya janye tallafi, ko kuma ya rufe ofishin jakadancin Amurka a duniya.

Wadannan masana dai suna ganin, ragewa ma’aikatar harkokin wajen kasar kudede masu yawa wanda ya kai dalar biliyon kimani 25, ya nuna cewa gwamnatin Amurka bata da wakilai a wasu wurare masu mihimmanci da dama a duniya, don haka ba zata sami labarin abinda yake faruwa a cikinsu ba. Kuma mai yuwa samun wadannan labarai suna da muhimmanci.

Wasu masu sukan suna ganin a halin da ake ciki mafi yawan kawayen Amurka, musamman kasashen turai sun tashi daga abokan aiki zuwa ga makiya ga gwamnatin Amurka. Sannan a kasashen masu tasowa, wadanda suke neman tallafi da taimako, Amurka ta bawa kasar China da Rasha dama ta su amfana da wadannan kasashe, ko basu bada kyauta ba, amma suna iya zuba jari a cikin kasashen inda bangarorin biyu zasu amfana.

A wani bangare kuma shugaban yana da shirin rage kudaden da ake kashewa ayyukan gwamnati a cikin gida, inda hakan ya kai ga rufe kafafen yada labarai da daman a gwamnatin Amurka. Hakan ya sa mutane da dama sun rasa ayyukansu a cikin kasar. Sannan daga kasashen waje ba, dubban ma’aikata sun rasa ayyukan daga kungiyoyin bada agaji ko kiwon lafiya ko tallafawa yara karkashin MDD wadanda gwamnatin Trump ta janye tallafin da suke bayarwa.

Daga karshe masana suna ganin, idan wannan halin ya ci gaba da alamun shugaba Donal Trump kama hanyar rusa kasar Amurka daga ciki da kuma wajen kasar a cikin shekaru 4 da zai yi a matsayin shugaban kasa. Mai yuwa gwamnatin da zata zo bayan tasa ta gaggauta gyaran wasu daga cikin abubuwan da ya bata. Amma wasu barnan da yayi ba zasu sake gyaruwa ba.

Don haka daga karshen dai Amurka ta kama hanyar wargajewa, idan ba an yi wani abu da gaggawa ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kungiyar BRICK Ta Rattaba Hannu A Kan Yarjeniyar Raya Ayyukan Noma A Duniya
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Manufar Kasarsa Da Shirin Kare Muradunta A Duk Wata Yarjejeniya
  • Iran ta yi ta’aziyya game da rasuwar Paparoma Francis
  • Putin ya rattaba hannu kan yarjejeniyar hadin gwiwa da Iran
  • Trump : “Mun yi ganawa mai kyau da Iran”
  • Sharhin Bayan labarai: Rage Kasafin Kudin Ma’ailatar harkokin wajen Amurka da tasirinsa
  • Shugaban Ma’aikatar Shari’a Yana Halartar Taro A Kasar China
  • Sharhi:  Kalankuwar  Kona Rayayyu Da Wuta A Gaza
  • NDLEA ta kama hodar iblis da aka ɓoye cikin littafai ana shirin kaiwa Saudiyya
  • Amurka : Ana ci gaba da zanga-zangar kyamar tsare -tsare da manufofin gwamnatin Trump