Ministan Harkokin Wajen Iran ya shawarci shugaban Amurka da ya mayar da yahudawan sahayoniyya zuwa Greenland

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya yi tsokaci kan kalaman shugaban Amurka Donald Trump da ya yi kan ba da shawarar korar Falasdinawa daga Zirin Gaza, maimakon haka Araqchi ya ba da shawarar kwashe ‘yan sahayoniyya Greenland.

Ministan harkokin wajen Iran ya yi ishara da haka ne a wata hira da kafar yada labarai ta Sky News, yana mai bayyana cewa: A mahangar ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran, a bayan da Trump ya shiga fadar White House a farkon wa’adinsa ya gabatar da shawarar korar Falasdinawa daga Zirin Gaza, amma kokarinsa ba ta yi nasara ba. hakan yana nufin rashin yiwuwar korar Falasdinawa daga tushensu.

Arqchi ya kuma mayar da martani ga tashar ta Sky News kan tambayar ‘yancin da ‘yan sahayoniyya suke da shi na rayuwa, inda ya ce: “Kowane dan Adam na da ‘yancin rayuwa, amma babu wanda ke da hakkin ya mamaye kasar wani, wannan kasa ta Falasdinawa ce, dole ne Falasdinawa su yanke shawara da kansu game da makomar kasarsu”.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Isra’ila na karbe yankuna a zirin Gaza

Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya bayyana cewa sojojin kasar na karbe iko da wasu yankunan zirin Gaza, a wani mataki na kara matsin lamba kan kungiyar Hamas domin tilasta ta sakin mutanen da ta ke garkuwa da su.

“Muna karbe zirin Gaza tare da kara matsin lamba mataki-mataki domin tilasta su mayar da mutanen da aka yi garkuwa da su,”inji  Netanyahu a wani faifan bidiyo da ofishinsa ya fitar.

Ya kara da cewa, Sojoji na karbe yankuna, suna kai farmaki kan ‘yan wadanda ya danganta da ‘yan ta’adda in ji shi, yana mai sanar da samar da wata sabuwar hanya karkashin ikon Isra’ila don raba garuruwan Khan Younis da Rafah (kudu).

Tunda farko dama ministan tsaron Isra’ila Israel Katz ya sanar a Larabar nan cewa, kasarsa ta fadada kaddamar da hare-haren soji a sassan zirin Gaza, yana mai barazanar dakarun Isra’ila za su kwace karin yankuna a zirin da nufin samar da yankuna masu tsaro da za su raba Isra’ila da wurare masu fama da tashin hankali.

Cikin wata sanarwa, mista Katz ya ce matakin fadada ayyukan sojin zai kunshi fadada kwashe mutane daga yankunan da ake dauki ba dadi a Gaza.

Isra’ila dai ta kawo karshen wa’adin tsagaita wuta na watanni 2 tun a ranar 18 ga watan Maris da ya shude, inda ta koma kaddamar da munanan hare-hare ta sama da kasa kan wuraren da Falasdinawa ke fakewa.

A jiya Talata, hukumomin lafiya a Gaza sun ce kawo yanzu sabbin hare-haren sun sabbaba rasuwar Falasdinawa 1,042 tare da jikkata wasu 2,542, yayin da rikicin da ya barke tun daga watan Oktoban shekarar 2023 zuwa yanzu, ya haddasa jimillar asarar rayukan Falasdinawa 50,399, tare da jikkata wasu 114,583.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila na karbe yankuna a zirin Gaza
  • Araghchi : Iran a shirye take don tattaunawa amma barazanar soji daga Amurka na dagula yanayin’
  • Gwamnatin Nijar, ta saki ministocin hambarariyar gwamnatin Bazoum
  • Shugaban Tinubu Ya Tube Kyara A Matsayin Shugaban Kamfanin NNPC Ya Kuma Sannan Ya Maye Gurbinsa
  • Tinubu ya cire Mele Kyari daga shugabancin NNPC
  • Ana Zaman Dar-dar A Kasar Zimbabwe Saboda Shirin Zanga-zangar Tsofaffin Sojaji
  • Kasar Sin Ta Nanata Adawa Da Matakan Tilastawa Da Nuna Babakeren Tattalin Arziki
  • Iran ta mayar wa Amurka martani kan barazanar kai mata hari
  • Iran ta gargadi Amurka kan barazanar harin bam da Trump ya yi
  • Iran Ta Ce Tattaunawa Da Amurka Tare Da Mai Shiga Tsakani Na Gaba, Ya Danganci Matakan Da Ta Dauka Kan Iran