Ministan Harkokin Wajen Iran ya shawarci shugaban Amurka da ya mayar da yahudawan sahayoniyya zuwa Greenland

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya yi tsokaci kan kalaman shugaban Amurka Donald Trump da ya yi kan ba da shawarar korar Falasdinawa daga Zirin Gaza, maimakon haka Araqchi ya ba da shawarar kwashe ‘yan sahayoniyya Greenland.

Ministan harkokin wajen Iran ya yi ishara da haka ne a wata hira da kafar yada labarai ta Sky News, yana mai bayyana cewa: A mahangar ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran, a bayan da Trump ya shiga fadar White House a farkon wa’adinsa ya gabatar da shawarar korar Falasdinawa daga Zirin Gaza, amma kokarinsa ba ta yi nasara ba. hakan yana nufin rashin yiwuwar korar Falasdinawa daga tushensu.

Arqchi ya kuma mayar da martani ga tashar ta Sky News kan tambayar ‘yancin da ‘yan sahayoniyya suke da shi na rayuwa, inda ya ce: “Kowane dan Adam na da ‘yancin rayuwa, amma babu wanda ke da hakkin ya mamaye kasar wani, wannan kasa ta Falasdinawa ce, dole ne Falasdinawa su yanke shawara da kansu game da makomar kasarsu”.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Iran Ya Aike Da Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Papa Roma Farancis

A yau Litinin shugaban kasar Iran Mas’ud Fizishkiyan ya fitar da sanarwa ta nuna aljinin rasuwar Papa Roma Farancis,sannan kuma ya mika sakon ta’aziyya ga Mabiya darikar Roman Katolika na duniya.

Shugaban kasar ta Iran ya rubuta cewa; Daga cikin matsaya da ta kasance fitacciya wacce Papa Roman ya dauka a lokacin rayuwarsa ita ce ta kalubalantar yadda ake take hakkin bil’adama a duniya, musamman mai dai yadda ya yi Allawadai da kisan kiyashin da ‘yan sahayoniya suke yi wa Falasdinawa a Gaza. Haka nan kuma yadda ya rika yin kira da HKI ta kawo karshen kisan kiyashin da take yi, da kashe mata da kananan yara.

Fizishkiyan ya kuma kara da cewa; Wadannan matakan da Papa Roman ya dauka a lokacin rayuwarsa za su wanzar da ambatonsa a cikin zukatan masu rayayyen lamiri da kuma wadanda suke yin kira da tabbatr da ‘yanci a duniya.

Shugaban kasar na Iran ta kitse sakon nashi da cewa; A madadin ni kaina da kuma  al’ummar Iran ina yin jinjina ga mamacin wanda ya yi fafutuka wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro a duniya.

A yau Litinin ne dai Fadar Vatican ta sanar da rasuwar Papa Roma Farancis wanda shi ne dan asalin yankin Latin na farko da ya jagoranci majami’ar .

Fadar ta kuma sanar da zaman makoki na kwanaki 9, sannan kuma ta sanar da cewa nan da makwanni biyu zuwa uku za a fara shirye-shiryen zabar sabon Papa Roma.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Manufar Kasarsa Da Shirin Kare Muradunta A Duk Wata Yarjejeniya
  • Wang Yi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Sabon Ministan Harkokin Wajen Sudan Ta Kudu
  • Sharhin Bayan labarai: Rage Kasafin Kudin Ma’ailatar harkokin wajen Amurka da tasirinsa
  • Shugaban Kasar Iran Ya Aike Da Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Papa Roma Farancis
  • Ministan HarkokinWajen Iran Ya Tattauna Da Takwarorinsa Na Swaitzerland Da Pakistan Ta Wayar Tarho
  • Kakakin Ma’aikatar Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Babban Abin Da Suke Bukata Shi Ne Daga Takunkumi
  • New York Times : Amurka na son rage ofisoshin jakadncinta a Afirka
  • Gobara ta ƙone gidaje sama da 100 a sansanin ’yan gudun hijira a Borno 
  • An Gayyaci Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Abbas Aragchi Taron Makamashin Nukliya A Amurka
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Yaba Da Zaman Tattaunawan Iran Da Amurka Zagaye Na Biyu A Birnin Roma