Gwamnatin Jigawa Ta Kaddamar Da Shirin Tallafawa Masu Kanana Da Matsakaitan Sana’o’i
Published: 30th, January 2025 GMT
Gwamnatin jihar Jigawa ta kashe sama da naira miliyan dubu dari da sittin da hudu wajen tallafawa kanana da matsakaitan masana’antu a jihar.
Gwamna Umar Namadi ya bayyana hakan a lokacin kaddamar da rabon katin cire kudi na ATM ga wadanda suka ci gajiyar shirin inganta rayuwar al’umma na gwamnatin tarayya da aka gudanar a sakatariyar karamar hukumar Dutse.
Malam Umar Namadi ya bayyana cewar, hukumar bunkasa tattalin arziki ta jihar ce ta fitar da ta hannun shirin farfadowa daga annobar cutar corona.
A cewar sa, kusan mutane dubu ashirin da uku ne za su amfana da tallafin naira dubu saba’in da biyar a jihar.
Yana mai cewar, hakan na daga cikin kudirin shugaban kasa na Renewed Hope agenda na tallafawa masu karamin karfi domin bunkasa tattalin arzikin su.
A don haka, Namadi ya yi kira ga wadanda za su cigajiyar shirin da su yi cikakken amfani da kudaden wajen inganta rayuwar iyalansu.
Wakilinmu ya aiko mana da rahoton cewar, wadanda suka yi jawabai sun hada da mataimakan Gwamnan jihar, Injiniya Aminu Usman da shugaban karamar hukumar Dutse da jami’in kula da shirin inganta rayuwar al’umma na jihar Alhaji Mustapha Umar Babura.
Wasu daga cikin wadanda suka amfana da tallfin sun yabawa Gwamnatin jihar da ta tarayya bisa bullo da shirin.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Janar Salami: Muna Cikin Shirin fuskantar Yaki A Duk Yadda Ya Zo
Kwamandan dakarun kare juyin musulunci na Iran Janar Husaini Salami ya bayyana cewa; Dangane da Shirin Nukiliyar Iran, muna bai wa diplomasiyya fifiko, amma kuma a lokaci daya muna cikin Shirin fuskantar kowane irin yaki duk yadda ya zo.
Janar Salami wanda ya gabatar da jawabi a wurin karrama shahidan yi wa kasa hidima, a hubbaren Imam Ridha ( a.s) ya kuma kara da cewa; Ya kamata Amurkawa su kwana da sanin cewa, idan su ka yi mana barazana, to a shirye muke domin fuskantar kowane irin yaki, a duk yadda ya zo.
Kwamandan dakarun kare juyin juya halin musuluncin na Iran ya kuma zargi Amrukawa da cewa su, ba masu cika alkawali ba ne, saboda yadda su ka yi wa Iran barazana da kuma kakaba mata sabbin takunkumai.
Janar Salami ya kuma ce; Jamhuriyar musulunci ba ta da azamar kera makamin Nukiliya bisa zabinta, ta kuma cire shi daga cikin akidarta ta tsaro.
Kwamandan dakarun kare juyin musuluncin na Iran ya kuma ce; Muna gargadin abokan gaba akan cewa idan har su ka tafka wani kuskure, to za a bude musu kofofin jahannama.
Janar Salami ya yi ishara da hare-haren “Wa’adussadiq 1, da na 2 da Iran ta kai wa HKI,sannan ya kara da cewa: Idan har ba za ku iya jurewa makami mai linzami guda daya daga Ansarullah jarumai daga Yemen ba, to yaya za ku yi da daruruwa da kuma dubban makamai masu linzami da za a harbo muku ?
Kwamandan na dakarun kare juyin juya halin musulunci na Iran ya yi jawabi akan cikar shekara da rasuwar shugaban kasa Ayatullah Ra’isi yana mai cewa; Ya kasance mutum wanda ya tattara soffofi na kamala, don haka ya cancanci yin shahada domin ita ce ta dace da shi.
Haka nan kuma ya yi jinjina ga shahidai irin su Kassim Sulaimani, Isma’ila Haniyyah, Yahya Sinwar, Sayyid Hassan Nasrallah, Safiyuddin, Zahidi, Musawi, ali-Hashim da kuma Rahmati.