Wata uku uami’o’i ba su da wutar lantarki —SSANU
Published: 30th, January 2025 GMT
Kungiyar Manyan Ma’aikatan Jami’a (SSANU) ta bayyana cewa jami’o’in gwamnati da dama a Najeriya sun shafe sama da watanni uku ba tare da wutar lantarki ba da za su gudanar bincike ko darussa ba.
Kungiyar ta kuma yi barazanar ɗaukar tsattsauran mataki kan gwamnatocin jihohi da kamfanoni da suka ki fara biyan sabon mafi ƙarancin albashi ba na Naira dubu 70 da sauran sauye-sauye da ke tattare da shi zuwa ƙarshen watan Maris na shekarar nan ta 2025.
Shugaban Ƙungiyar SSANU ta Kasa, Kwamred ohammed Ibrahim, ne ya sanar da haka a yayin taron Majalisar Tuntuba ta Ƙasa (NAC) da ƙungiyar ta gudanar a Abuja.
Kwamred Ibrahim ya bayyana cewa har yanzu Gwamantin Tarayya da na wasu jihohi ba su fara biyan ma’aikatan jami’a sabon albashin ba, duk da kasancewarsu ƙwararru a fannoni daban-daban.
Game da zargin ’yan Majalisar Dokoki ta Ƙasa da neman xin hancin Naira miliyan takwas daga kowane shugaban jami’ar Gwamnatin Tarayya kafin su amince da kasafin kuɗin makarantarsa, ƙungiyar ta ce idan har hakan ta tabbata, to za su yaƙi lamarin kai da fata.
Ya ƙara da “idan ta tabbata, to wannan babban abin takaici ne, don a halin yanzu babu wata jami’ar gwamnati da ake da isassun kuɗaɗen biyan kuɗin lantarki.
“Daga cikinsu akwai waɗanda rabonsu da amfani da wutar an fi wata uku. Ta daga ina za su samu kudin da za su ba ’yan majalisar cin hanci Naira miliyan takwas-takwas.
“Idan har wakilan da jama’a suka zaɓa domin su tabbatar da cewa makarantun sun samun cikakkiyar kulawa babu tauyewa ne za su dawo suna neman cin hanci daga wurinsu, lallai za mu ɗauki mataki.
“Ina tabbatar maka cewa majalisa ba ta fi ƙarfinmu ba, za mu yaƙe su, domin a mazaɓunmu suke, za samu kayar da su,” in ji shugaban na ma’aikatan jami’a.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Wutar Lantarki
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda ma’aikatan gidan ruwa 4 suka mutu a Bauchi
Ma’aikatan Hukumar Samar da Ruwan Sha ta Jihar Bauchi guda huɗu sun rasu a yayin da suke aikin tsabtace madatsar ruwa ta Gubi.
Wasu jami’ai da ke aiki a Madatsar Ruwa ta Gubi, sun bayyana cewa daga cikin mamatan har da wani uba da dansa da kuma wani wanda ke shirye-shiryen ɗaurin aurensa.
“Abin ya faru ne a lokacin da suke aikin tsaftace ruwan da ake kula da ruwan da ake yi wa babban birnin Bauchi. Na samu labarin suna cikin tafki, sai suka ga wasu kifaye a cikin ruwan datti, ɗaya daga cikinsu yana ƙoƙarin kama kifi, kifin ya yi zurfi, sai ya bi shi ya mutu.
“Ana cikin haka, wani abokin aikinsa da ya ga abin da ya faru ya yi ƙoƙarin ceto shi, shi ma ya mutu, kuma anyi musu jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ta tanada,” kamar yadda wani abokin aikinsu ya bayyana.
Ambaliya ta kashe mutum 3 ta lalata hekta 10,000 na shinkafa a Neja Ango ya tsere tare da surukarsa Gobara ta ƙone gidaje sama da 100 a sansanin ’yan gudun hijira a BornoKakakin Rundunar ’Yan Sanda a Jihar Bauchi, CSP Mohammed Ahmed Wakil ya ce ma’aikatam da suka rasu sun hada Shayibu Hamza mai shekaru 48 da Abdulmalik Yahya mai shekaru 29 da Jamilu Inusa mai shekaru 29 da kuma Ibrahim Musa mai shekaru 42.
Ya ci gaba da cewa lamari mai ban tausayi ya auku a madatsar ruwa ta Gubi, wanda ya yi sanadin asarar ma’aikatan da suka sadaukar da kansu a yayin wani aikin yashe shara da ke cikin ramuka a madatsar ruwan ta Gubi.
Ya ce A lokacin da waƙi’ar ta auku, an yi ƙoƙarin ceto su, aka fito da su a sume daga cikin ramin tara ruwan da suke aikin, daga nan aka garzaya da su Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Ɓalewa da ke Bauchi, amma duk da kulawar gaggawa da aka ba su, sai Allah Ya karɓe su, likitoci suka tabbatar da rasuwarsu.
Wakil ya ce, a lokacin da ’yan sanda suka samu labarin faruwar lamarin, sun tura jami’ai zuwa wurin, yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike don gano ainihin abin da ya faru.
Ya ce akwai buqatar qara daukan matakai a vangaren kula da ruwa, yana mai jaddada muhimmancin dukkan ma’aikatan su kula da bin ƙa’idojin aminci da aka kafa don rage haɗari nan gaba.
Duk ƙoƙarin da muka yi na jin ta bakin Kwamishinan Albarkatun Ruwa ma Jihar Bauchi, Abdulrazaq Nuhu Zaki, da Babban Manajan Kamfanin Samar da Ruwan Sha na Jihar Bauchi, Injiniya Aminu Aliyu Gital, a game da lamarin ya ci tura.