Wata uku uami’o’i ba su da wutar lantarki —SSANU
Published: 30th, January 2025 GMT
Kungiyar Manyan Ma’aikatan Jami’a (SSANU) ta bayyana cewa jami’o’in gwamnati da dama a Najeriya sun shafe sama da watanni uku ba tare da wutar lantarki ba da za su gudanar bincike ko darussa ba.
Kungiyar ta kuma yi barazanar ɗaukar tsattsauran mataki kan gwamnatocin jihohi da kamfanoni da suka ki fara biyan sabon mafi ƙarancin albashi ba na Naira dubu 70 da sauran sauye-sauye da ke tattare da shi zuwa ƙarshen watan Maris na shekarar nan ta 2025.
Shugaban Ƙungiyar SSANU ta Kasa, Kwamred ohammed Ibrahim, ne ya sanar da haka a yayin taron Majalisar Tuntuba ta Ƙasa (NAC) da ƙungiyar ta gudanar a Abuja.
Kwamred Ibrahim ya bayyana cewa har yanzu Gwamantin Tarayya da na wasu jihohi ba su fara biyan ma’aikatan jami’a sabon albashin ba, duk da kasancewarsu ƙwararru a fannoni daban-daban.
Game da zargin ’yan Majalisar Dokoki ta Ƙasa da neman xin hancin Naira miliyan takwas daga kowane shugaban jami’ar Gwamnatin Tarayya kafin su amince da kasafin kuɗin makarantarsa, ƙungiyar ta ce idan har hakan ta tabbata, to za su yaƙi lamarin kai da fata.
Ya ƙara da “idan ta tabbata, to wannan babban abin takaici ne, don a halin yanzu babu wata jami’ar gwamnati da ake da isassun kuɗaɗen biyan kuɗin lantarki.
“Daga cikinsu akwai waɗanda rabonsu da amfani da wutar an fi wata uku. Ta daga ina za su samu kudin da za su ba ’yan majalisar cin hanci Naira miliyan takwas-takwas.
“Idan har wakilan da jama’a suka zaɓa domin su tabbatar da cewa makarantun sun samun cikakkiyar kulawa babu tauyewa ne za su dawo suna neman cin hanci daga wurinsu, lallai za mu ɗauki mataki.
“Ina tabbatar maka cewa majalisa ba ta fi ƙarfinmu ba, za mu yaƙe su, domin a mazaɓunmu suke, za samu kayar da su,” in ji shugaban na ma’aikatan jami’a.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Wutar Lantarki
এছাড়াও পড়ুন:
Kasar Sin Za Ta Yi Ramuwar Gayya Kan Takunkumin Biza Da Amurka Ta Kakaba Wa Jami’anta
A yau Talata, kasar Sin ta bayyana cewa, za ta dauki matakan ramuwar gayya domin mayar da martani game da sanarwar da Amurka ta fitar ta saka takunkumin biza a kan jami’an kasar Sin, bisa hujjar hana izinin shiga yankin Xizang mai cin gashin kansa, da ke kudu maso yammacin kasar Sin.
A yayin taron manema labarai da aka saba yi a-kai-a-kai, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Guo Jiakun ya bayyana cewa, yankin Xizang a bude yake ga kowa da kowa, kuma ba a hana baki daga kasashen waje shiga ba, inda ya kara da cewa, yankin yana karbar dimbin matafiya da sauran al’ummomi da dama daga sassa daban-daban a kowace shekara, domin ko a shekarar 2024 kadai, akalla baki 320,000 ne suka shiga yankin.
Jami’in ya ce, kasar Sin tana kira ga Amurka da ta mutunta alkawuran da ta dauka kan batutuwan da suka shafi Xizang, da daina hada baki ko goyon bayan masu gwagwarmayar “’yancin kai” na Xizang, da kuma dakatar da amfani da batutuwan da suka shafi Xizang wajen yin katsalandan a harkokin cikin gidan kasar Sin. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp