HausaTv:
2025-04-26@06:41:32 GMT

Gabashin DRC : Félix Tshisekedi Ya Sanar Da Maida Da Martani”

Published: 30th, January 2025 GMT

Shugaba Felix Tsisekedi na Jamhuriyar Demokuradiyyar Congo ya bukaci hadin kai na al’ummar kasar tare da sanar da mayar da martini kan rikicin gabashin kasar dake da nasaba da kungiyar ‘yan tawaye ta M23.

A yayin wani jawabi ga al’ummar kasar, shugaban na Kongo ya yi kira da a hada kai tare da ba da tabbacin cewa “ana ci gaba da mayar da martini kuma an karfafa tsarin tsaro.

” Ya kuma yi tir da gazawar kasashen duniya da kasancewar dubban sojojin Rwanda a kasar tare da bayyana kungiyar ta M23.

Wannan dai shi ne karon farko da shugaban na Kwango ke magana tun bayan harin da ‘yan tawayen suka kai a gabashin kasar a garin Goma.

Yayin jawabin shugaban na Kwango ya kuma ce suna goyon bayan hanyar tattaunawa.”

Félix Tshisekedi ya kuma yaba wa sojojin da suka fadi a fagen daga.”

Kungiyar M23 da ke samun goyon bayan sojojin Rwanda kimanin 3,000 zuwa 4,000, a cewar MDD, ta shafe fiye da shekaru uku tana fafatawa da sojojin Kongo a yankin, amma sun kutsa a cikin Goma babban birnin gabashin kasar a daren ranar Lahadi  zuwa Litinin ga watan Janairun nan inda suka mamaye tsatsa dama.

Akalla mutane 100 ne suka mutu sannan wasu sama da 1,000 suka jikkata, a cewar rahotanni daga asibitoci da dama.

Halin da ake ciki na jin kai yana da matukar damuwa, in ji Majalisar Dinkin Duniya, inda ta sanar da cewa dole ne a dakatar da rarraba kayan agaji saboda yanayin tsaro.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Ce Ya Kamata Amurka Ta Tattauna Da Ita Bisa Mutuntawa Matukar Da Gaske Take

Jami’in ya kara da cewa, kasar Sin ba ta son gwabza yakin kasuwanci da karin harajin kwastam, amma kuma ba za ta rungume hannu ta zuba ido ba idan yakin ya kaure, yana mai nuni da cewa, idan har Amurka ta zabi fafata yakin kasuwanci, Sin za ta sha damarar yakin har sai ta ga abin da ya ture wa buzu nadi. Sai dai kuma duk da haka, ya ce idan Amurka na son a tattauna, Sin za ta bar kofarta a bude domin yin hakan.

 

Bugu da kari, dangane da batun yadda a baya-bayan nan kafafen yada labarun kasar Panama suka soki Amurka kan yin katsalandan da nuna babakere a kasashen yankin tsakiyar Amurka, musamman a kasar ta Panama, inda suka zargi Amurkar da yunkurin karbe ragamar mashigin ruwan Panama ta hanyar fakewa da wai “barazanar kasar Sin” wadda babu ita kwata-kwata. Guo Jiakun ya mayar da martani inda ya ce, bayanan da kafafen yada labarai na Panama suka yi sun fallasa ainihin halin Amurka na babakere.

 

Guo ya kara da cewa “Babu wata karya da za ta iya lullube ungulu da kan zabon Amurka a kan burinta na neman karbe akalar mashigin ruwan Panama”. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Ta Goyi Bayan Rawar Da Hukumar IAEA Ke Takawa Wajen Warware Batun Nukiliyar Iran Ta Hanyar Diflomasiyya
  • Shugaban Amurka Ya Ce: Natenyahu Ba Zai Hadi Fada Da Jamhuriyar Musulunci ta Iran Ba
  • An kama mutane 13 kan zubar da ciki a Bauchi
  • Sojonin Yemen Ta Kakkabo Jiragen Yakin Amurka Wadanda Kimarsu Ya Dalar Amurka Miliyon $200 A Makonni 6
  • Sharhin Bayan Labarai: Shin Kissan Mutanen Gaza Gaba Daya
  • Uwargidan Shugaban Kasar Sin Ta Tattauna Da Takwararta Ta Kasar Kenya
  • Congo Da M23 Sun Cimma Yarjejeniyar Tsagaita Wuta
  • An Umurci Sojoji Su Kawarda ‘Yan Bindiga Daga Kwara Da Niger A Cikin Wata Daya
  • Sin Ta Ce Ya Kamata Amurka Ta Tattauna Da Ita Bisa Mutuntawa Matukar Da Gaske Take
  •  Ghana Ta Fada Cikin Takaddama Bayan Tisge Babbar Mai Shari’a Ta Kasar Da Shugaban Kasa Ya Yi