HausaTv:
2025-04-02@18:45:55 GMT

ECOWAS : Kofarmu A Bude Take Ga Al’ummun Kasashen Burkina, Mali Da Nijar

Published: 30th, January 2025 GMT

Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka (ECOWAS) ta ce kofar kasashe mambobinta a bude take domin shige da ficen al’ummun kasashen kawancen Sahel da suka balle daga cikinta wato Burkina Faso, Mali da Nijar.

A wata sanarwar da ta fitar ranar Laraba a shafinta na X, ECOWAS ta ce duk da cewar daga ranar Laraba 29 ga watan Janairun shekarar 2025 ne ficewar kasashen daga ECOWAS ta tabbata, tana kira ga kasashe mambobinta su saurara wa al’ummmun kasashen uku.

Sanarwar ta ce saboda hadin kai na yankin da amfanin jama’a da kuma shawara da muhukuntan ECOWAS suka yanke ta barin kofar kungiyar a bude, ECOWAS za ta ci gaba da amincewa da fasfo din ‘ya’yan kasashen da ke dauke da tambarin ECOWAS.

Ta kara da cewa ta nemi dukkan ƙasashen ECOWAS su ci gaba da bin tsarin sassaucin kasuwanci bisa shige da fice na kayayyaki da ma’aikata daga kasashen AES zuwa kasashen ECOWAS.

Kazalika ECOWAS ta nemi kasashen su ba da hadin kai ga jami’an ECOWAS daga kasashen a ciki aikin su ga ECOWAS, har zuwa lokacin da shugabannin kasashen ECOWAS za su yanke shawara game da irin huldar da za su yi da kasashen uku.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sarkin Gombe ya nemi manoma da makiyaya su zauna lafiya

A Bikin Yawan Sallah na Jafi da aka yi a fadar Sarkin Gombe, Mai Martaba Alhaji Abubakar Shehu Abubakar III, ya yi kira ga manoma da makiyaya da su zauna lafiya da juna.

Sarkin ya ce zaman lafiya shi ne ginshiƙin ci gaba, kuma haɗin kai tsakanin manoma da makiyaya zai hana rikice-rikice da ke barazana ga jihar.

Matashi ya kashe jami’in tsaron Sarki Sanusi II a Kano Gwarzon gasar Alƙur’ani ya kuɓuta daga hannun ’yan bindiga a Katsina

“Ina roƙon manoma da makiyaya da su zauna lafiya don guje wa rigingimu.

“Kowa yana da haƙƙin tabbatar da zaman lafiya domin hakan na kawo ci gaban tattalin arziƙi da walwalar al’umma,” in ji Sarkin.

Haka kuma, ya tabbatar da cewa masarautar Gombe za ta ci gaba da goyon bayan gwamnatin jihar domin tabbatar da tsaro mai ɗorewa.

Sarkin ya gode wa Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, bisa ƙoƙarinsa na inganta rayuwar al’umma da ɗaukar matakan tsaro, musamman samar da motocin aiki ga jami’an tsaro.

Bikin hawan sallah na Jafi ya samu halartar manyan baƙi, ciki har da Gwamnan Jihar Gombe da wasu manyan jami’an gwamnati, inda aka jaddada buƙatar haɗin kai da zaman lafiya a jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • DG VON Yayi Kira Ga Zaman Lafiya Da Hadin Kai Don Fadada Ci gaban Tattalin Arziki Da Ci Gaba.
  • Tsohon Gwamnan Zamfara Ya Bukaci A Ci Gaba Da Tallafawa Mabukata Bayan Ramadan.
  • Nijar Ta Fice Daga Rundunar Tsaro Ta Haɗin Kai MNJTF
  • Jagora : A yau, duniyar musulmi tana bukatar hadin kai
  • Jakadan Kasar Sin Ya Bukaci Hadin Gwiwar Inganta Amfani Da AI Don Amfanar Da Kowa
  • A Yau Litinin Ce Aka Gudanar Da Sallar Edi Da Bukukuwan Sallah A Nan Iran Da Wasu Kasashen Musulmi
  • Nijar ta fice daga rundunar MNJTF mai yaƙi da masu iƙirarin jihadi
  • Kasar Sin Ta Jaddada Bukatar Karfafa Cinikayya Da Ketare Tare Da Fadada Bude Kofa
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci: Kasashen Yamma Sune Yan Ta’adda Na Gasliya A Yankin
  • Sarkin Gombe ya nemi manoma da makiyaya su zauna lafiya