Kungiyar fursunonin Falasdinu ta ce za a sako wasu karin Falasdinawa 110 daga gidajen yarin Isra’ila a yau Alhamis a mataki na uku na yarjejeniyar tsagaita bude wuta da musayar fursunoni tsakanin Isra’ila da Hamas.

Ana sa ran galibin Falasdinawan da aka ‘yantar za su isa yankin Radana na Ramallah da ke yammacin gabar kogin Jordan da aka mamaye da misalin karfe 12:00 na safe agogon kasar, in ji kungiyar fursunonin Falasdinu.

Wannan ba zai hada da fursunoni 20 da za a tura gudun hijira a wajen Falasdinu ba.

Kungiyar ta kuma fitar da jerin sunaye da shekarun fursunonin da za a saki wadanda suka hada da akalla yara 30.

Sakin da za’ayi wa Falasdinawan 110 a yau zai sanya adadin Falasdinawa da aka sako daga gidajen yarin Isra’ila zai kai 400 yayin da ake aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin bangarorin biyu duk da cewa Isra’ila na ci gaba da keta yarjejeniyar ta hanyar kai farmaki da samame.  

Ko a baya baya bayan nan sojojin Isra’ilar sun kame wasu Falasdinawa da dama a yankin yammacin gabar kogin Jordan, ciki har da Falasdinawa 12 da aka kama a gabashin Kudus.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Hamas Ta Bukaci Falasdinawa A Birnin Qudus Su Sabawa Dokar Takaita Yawan Masu Shiga Masallacin Al-Aksa A Kudus

Wata kungiyar kare hakkin bil’adama ta kasa da kasa ta bada rahoton cewa sojojin HKI sun kashe akalla yara 16 tun farkon wannan shekara ta 2025 a yankin yamma da kogin Jordan.

Tashar talabijin ta Presstv  a nan Tehran ta nakalto Ayed Abu Eqtaish, daraktan kungiyar ‘ The Defense for Children International’ a yankin yamma da kogin Jordan yana fadar haka. Ya kuma zargi manya manyan kasashen duniya da kyale gwamnatin HKI tana aikata irin wadannan laifuka kan Falasdinawa a gaban idan kowa.

Eqtaish ya kara da cewa, rashin magana da kuma takawa gwamnatin yahudawan birki yana sa ta kara yawan kashe yara Falasdinawa a duk sanda ta ga dama.

Kafin haka wani rahoton MDDya bayyana cewa idan ba’a hana HKI da karfi ba, to ba za ta takaita kisan kiyanshi a Gaza kadai ba, zata fadadashi zuwa yankin yamma da kogin Jordan.

Sojojin HKI sun ta aikata kissan kiyashi a gaza a yain fin karfin da ta yi a Gaza na tsawon watanni 15, inda ta kashe fal;asdinawa fiye da 61,000 kafin a tsagaita wuta a ranar 19 ga watan Jenerun da ya gabata.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masar Za Ta Bayyana Shirin Sake Gina Gaza A Yayin Taron Larabawa
  • Hamas: Matakin Netanyahu na hana shigar kayan agaji a Gaza keta yarjejeniyar tsagaita wuta ne
  •  Hamas: Matakin Netenyahu Na Dakatar Da Shigar Kayan Agaji Cikin Gaza Keta Yarjejeniya Ne
  • Hamas Ta Bukaci Falasdinawa A Birnin Qudus Su Sabawa Dokar Takaita Yawan Masu Shiga Masallacin Al-Aksa A Kudus
  • Motocin Buldoza Suna Ta Rusa Gidajen Falasdinawa A Yankin Yamma Da Kogin Jordan
  • Hamas Ta Yi Watsi Da Shawarar Isra’ila Na Tsawaita Matakin Farko Na Tsagaita Wuta A Gaza
  • Al-Houthi : Isra’ila Na fakewa Da Goyan Bayan Amurka Tana Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza
  • Kasashen Afirka ta Kudu da Malaysia da Colombiya za su hana jiragen ruwa da ke dauke da makamai zuwa Isra’ila
  • Kasashen Afrika Ta Kudu, Malasiya Da Colombia Zasu Hana Jiragen Ruwa Dauke Da Makamai Tsayawa A Tashoshin Jiragen Ruwansu
  • An kori ma’aikatan Microsoft saboda adawa da yahudawan sahyoniya