Gaza : Za’a Sako Falasdinawa 110 A Wannan Alhamis A Musayar Fursunoni Da Isra’ila
Published: 30th, January 2025 GMT
Kungiyar fursunonin Falasdinu ta ce za a sako wasu karin Falasdinawa 110 daga gidajen yarin Isra’ila a yau Alhamis a mataki na uku na yarjejeniyar tsagaita bude wuta da musayar fursunoni tsakanin Isra’ila da Hamas.
Ana sa ran galibin Falasdinawan da aka ‘yantar za su isa yankin Radana na Ramallah da ke yammacin gabar kogin Jordan da aka mamaye da misalin karfe 12:00 na safe agogon kasar, in ji kungiyar fursunonin Falasdinu.
Wannan ba zai hada da fursunoni 20 da za a tura gudun hijira a wajen Falasdinu ba.
Kungiyar ta kuma fitar da jerin sunaye da shekarun fursunonin da za a saki wadanda suka hada da akalla yara 30.
Sakin da za’ayi wa Falasdinawan 110 a yau zai sanya adadin Falasdinawa da aka sako daga gidajen yarin Isra’ila zai kai 400 yayin da ake aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin bangarorin biyu duk da cewa Isra’ila na ci gaba da keta yarjejeniyar ta hanyar kai farmaki da samame.
Ko a baya baya bayan nan sojojin Isra’ilar sun kame wasu Falasdinawa da dama a yankin yammacin gabar kogin Jordan, ciki har da Falasdinawa 12 da aka kama a gabashin Kudus.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Faransa : An kama wata ‘yar Iran mai goyon bayan Falasdinu
A faransa ana ci gaba da tsare wata ‘yar Iran mai goyan bayan Falasdinu, bis azarginta da iza ta’addanci.
Mahdieh Esfandiari (mai shekaru 35) ana tsare da ita tun ranar 28 ga watan Fabrairu, bayan kama ta a binrin Lyon, inda ta ke da zama.
Iran ta bakin kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar, Esmail Baghai, ya yi Allah wadai da kama Mahdieh Esfandiari, yana mai yin Allah wadai da “manufofin kasashen Turai” wanda “ya kunshi murde adawa da “kisan kare dangi” da Isra’ila ta yi a Gaza.
Ya kara da cewa ba a sanar da ofishin jakadancin Iran da ke birnin Paris da kuma iyalan yarinyar ba.
A nasa bangaren, lauyan Mahdieh Esfandiari, Nabil Boudi, ya nuna rashin jin dadinsa kan kamun da aka yi wa wadda yake karewa.