HausaTv:
2025-03-03@09:29:36 GMT

Nukiliya : Babu Wani ‘Musayar Sako’ Tsakaninmu Da Amurka_ Araghchi  

Published: 30th, January 2025 GMT

Ministan harkokin wajen Iran ya ce Tehran ba ta samu wani sako daga sabuwar gwamnatin Amurka dangane da tattaunawar janye takunkumin ba.

Abbas Araghchi ya fada a ranar Laraba cewa duk wani matakin shiga irin wannan tattaunawa ya ta’alaka kan kwarin gwiwar da gwamnatin Donald Trump take da shi.

Ministan ya ce Iran ta riga ta shiga tattaunawa da bangarorin Turai da ke cikin yarjejeniyar nukiliyar ta 2015, kuma tana jiran Washington ta fayyace manufofinta.

“Ba a aika ko karbo wani sako na musamman ba tsakanin kasashen biyu ba; saidai abubuwan da muke ji a kafafen yada labarai kawai.”

An yi ta rade-radin cewa gwamnatin Trump ta yi musayar sakonnin sirri da Iran.

“A baya mun cimma yarjejeniya; Iran ta aiwatar da ita, amma su ne suka kawo cikas,” in ji Araghchi, yana mai nuni da ficewar Amurka daga yarjejeniyar a shekarar 2018 a wa’adin mulkin farko na Trump.

Bayan ficewarta ne kuma gwamnatin Amurka ta kakabawa Iran sabbin takunkumai a wani mataki na matsin lamba ga Iran, lamarin da ya fusata Iran ta shiga tafiye-tafiyenta tare da soke aiki da wasu bangarori na yarjejeniyar ciki har da tace urenium din dinta son rai.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Zelensky : Ban Ga Laifin Da Na Yi Wa Trump, Ballantana In Nemi Afuwa

Shugaban Ƙasar Ukraine, Volodymyr Zelensky ya ce bai ga laifin da ya yi wa Shugaban Amurka Donald Trump, ballantana ya nemi afuwa.

Zelensky ya bayyana haka ne bayan zazzafar cacar-baki da ya kaure a tsakaninsa da Trump a ofishin shugaban ƙasar Amurka.

A cewarsa, “ina godiya ga Amurka da gudunmuwar da take ba mu,” in ji shi kamar yadda ya bayyana a hirarsa da Fox News.

Sai dai ya bayyana cewa musayar yawun ba ta dace ba, sannan ya kara da cewa dangantakar da ke tsakaninsa da Trump za ta gyaru.

Tunda farko dai an soke taron manema labarai da aka shirya yi a fadar White House a jiya Juma’a, inda shugaban Amurka Donald Trump da shugaban Ukraine Volodymyr Zelensky suka shirya rattaba hannu kan yarjejeniyar ma’adinai tsakanin Amurka da Ukraine, bayan wani sa-in-sa mai zafi tsakaninsu biyun a ofishin Trump wato Oval office a safiyar ranar.

Bayan musayar yawun da aka yi a ofishin, Trump ya wallafa wata sanarwa a dandalin sada zumunta na Truth, yana mai cewa, “Na yanke shawarar cewa Shugaba Zelensky bai shirya ma zaman lafiya idan da hannu Amurka a ciki ba. Ya ci mutuncin kasar Amurka a cikin Oval office mai daraja. Zai iya dawowa idan ya shirya ma zaman lafiya.”

A nasa bangaren, Zelensky ya wallafa a dandalin sada zumunta na X cewa, “Zaman lafiya mai dorewa Ukraine ke bukata, kuma muna aiki don samun hakan.”

Haka zalika, shugabar Majalisar Tarayyar Turai Roberta Metsola ta bayyana a dandalin sada zumunta na X cewa, “Za mu ci gaba da yin aiki tare da kai don samun zaman lafiya mai dorewa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran: Majalisar dokoki ta tsige ministan tattalin arziki saboda hauhawar farashi
  • Hamas: Matakin Netanyahu na hana shigar kayan agaji a Gaza keta yarjejeniyar tsagaita wuta ne
  • Masar ta ki amincewa da duk wani yunkuri na kafa gwamnatin ‘yan adawa a Sudan
  • Nijar: An Kashe Sojoji 11 A Wani Hari Na Kungiyar al-Ka’ida
  • Zelensky : Ban Ga Laifin Da Na Yi Wa Trump, Ballantana In Nemi Afuwa
  • Al-Houthi : Isra’ila Na fakewa Da Goyan Bayan Amurka Tana Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza
  • An Yi Musayar Yawu A Tsakanin Shugabannin Kasashen Amurka Da Ukiraniya A Fadar White House
  • Taron Kara Wa Juna Sani Kan Canton Fair Ya Ja Hankalin Masu Masana’antu Da ‘Yan Kasuwan Habasha
  • Babu Wani Dan Arewa Mai Hankali Da Zai Yi Wa APC Kamfen A 2027 – PDP
  • GORON JUMA’A