Aminiya:
2025-03-03@10:10:14 GMT

Kungiyar NLC ta kira zanga-zanga kan ƙarin kuɗin waya

Published: 30th, January 2025 GMT

Kungiyar Ƙwadago ta Ƙasa (NLC) ta kira zanga-zangar adawa da ƙarin data da kiran waya a Najeriya.

NLC ta umarci rassanta na jihohi 36 da Babban Birnin Tarayya da su shirya domin fara zanga-zangar daga ranar Takara 4 ga watan Fabrairu mai kamawa.

Ta bayyana cewa manufar zanga-zangar ita ce ganin an janye karin kashi 50% da aka yi wa kuɗin kiran waya da na data, da kuma adawa da tsadar rayuwa wadda ta jefa ’yan Najeriya cikin tasku.

Shugaban ƙungiyar, Joe Ajaero, ya bayyana cewa zanga-zangar zai zama gargaɗi ga shugabanni kan dore wa al’umma abin da bai dace ba sa rashin adalci.

“Wannan gangami zai yaƙi ƙare-ƙaren ganin dama rashin adalci da aka yi na man fetur da wutar lantarki da hauhawan farashin kaya alhali an bar mutane da albashin N70,000 wanda bai taka kara ya karya ba,” in ji shi.

Ya ci gaba da cewa, duk rassan NLC da ƙungiyoyin fararen hula da dangoginsu a shirye suke su shiga wanan yakjn aiki.

Don haka ya buƙaci hukumar sadarwa ta ƙasa da majalisar dokoki ta kasa su tattauna da masu ruwa da tsaki domin samun maslaha kan ƙarin kuɗin da suka tsara.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yajin aiki zanga zangar

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya sanya hannu a kasafin kuɗi na N54.99trn

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya sanya hannu kan kasafin kuɗin shekarar 2025 da ya kai Naira tiriliyan 54.99.

A ranar 13 ga watan Fabrairu, 2025, Majalisar Dokoki ta amince da kasafin bayan tattaunawa da nazari a kansa.

Hukuma ta kama ciyaman kan zargin badaƙalar filin N100m a Kano Gwamnatin Sakkwato ta nemi malaman Jami’a su janye yajin aiki 

A baya dai, Shugaba Tinubu ya gabatar da kasafin da ya kai Naira tiriliyan 49.7, amma daga bisani aka ƙara adadin kuɗin.

Shugaba Tinubu ya rattaba hannu kan kasafin a ranar Juma’a, a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

Kasafin kuɗin na 2025 ya ninka wanda aka yi a bara, wanda ya tsaya a Naira tiriliyan 27.5, da ƙarin kashi 99.96 cikin 100.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ta ina Kungiyar Hizbullah ke samun kuɗaɗenta?
  • An kama ɓarayin waya a Kano
  • Al-Houthi : Isra’ila Na fakewa Da Goyan Bayan Amurka Tana Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza
  • Yemen Ta Ce A Shirye Take Ta Koma Yaki Idan Yaki Ya Sake Barkewa A Gaza
  • ‘Yansanda Na Farautar Wadanda Suka Kashe Dalibi A Katsina
  • Ramadan: Ga arahar kayan abinci ga rashin kuɗin saya
  • Tinubu ya sanya hannu a kasafin kuɗin 2025 na N54.99trn
  • Tinubu ya sanya hannu a kasafin kuɗi na N54.99trn
  • Hukumar Lamuni Ta Duniya IMF Da Bankin Duniya Sun Ce Bazasu Taimakawa Lebanon Ba Sai Da Sharudda
  • Kungiyar Kare Hakkin Bil’adama ta ‘Euro-Med Monitor’ Ta Ce Ta Sami Shaidu Wadanda Suka Tabbatar Da Cewa HKI Tana Azabtar Da Fulasdinwa