Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-04-02@22:13:56 GMT

Hisbah Ta Kama Wasu Ma’aurata Da Suka Yi Aure A Asirce

Published: 30th, January 2025 GMT

Hisbah Ta Kama Wasu Ma’aurata Da Suka Yi Aure A Asirce

Hukumar Hisbah ta damke wasu matasa a jihar Kano bisa laifin yin aure a asirce ba tare da sanin iyayensu ko amincewar iyayensu ba.

A cewar Sheikh Mujahid Aminudeen Abubakar mataimakin kwamandan hukumar Hisbah ta jihar Kano, ma’auratan sun yi aure ne a wani wurin shakatawa bayan wani ya  dauki nauyin biyan sadaki.

Abubakar ya yi Allah-wadai da wannan  auren, inda ya bayyana shi a matsayin wanda bai dace da addinin Musulunci ba, kuma ba a yarda da shi ba.

“Hukumar ta kama ma’auratan kuma za ta ci gaba da bincike tare da kame abokansu da kuma wadanda suka taimaka wajen auren sirri.”

Abubakar ya yabawa wadanda suka sanar da hukumar auren sirri, sannan ya bukaci jama’a da su kai rahoton duk wani abu da ba a yarda da shi ba+ ga hukumomin da abin ya shafa.

Gidan Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, hukumar Hisbah ta jihar Kano na ci gaba da tabbatar da bin doka da oda a jihar.

Daga Khadija Aliyu

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Babu dokar da na karya saboda yin taro a mazaɓata — Natasha

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan da Majalisar Dattawan Nijeriya ta dakatar, ta ce taron barka da sallah da ta yi a mazaɓarta a yammacin Talata duk da haramta taruka da gwamnatin jihar ta yi ba karya doka ba ne.

Ana iya tuna cewa Gwamnatin Kogin dai ta hana duk wani nau’in taro ko gangami a jihar, saboda dalilin da ta ce na tsaro ne.

Haaland zai yi jinyar mako bakwai — Guardiola HOTUNA: Sarki Sanusi ya kai wa Abba ziyarar barka da Sallah

Kwamishinan ‘Yan sandan jihar, Miller Ɗantawaye, ya ce hana taron ya biyo bayan bayanan sirri da suka samu cewa za a samu barzanar tsaro, wanda ya tilasta gwamnatin jihar ɗaukar matakin.

Sai dai Natasha wadda ta isa jihar a wani jirgi mai saukar ungulu, ta bayyana wa magoya bayanta cewa tana da ’yancin kasancewa da mutanenta ta kuma yi shagalin farin ciki tare da su.

“A duk abin da za mu yi, mu sanya Allah a farko kuma mu shigar masa da buƙatunmu ta hanyar addu’a.

“Mijina ya kasance ɗaya daga cikin addu’o’ina da Allah Ya amsa. In banda haka ta yaya ni da ba kowa ba ce fa ce talaka daga ƙabilar Ebira na samu ƙarfin samun jirgin da zai kawo ni gida?

“Goyon bayan mijina ne ya kawo haka, kuma shi ke ciyar da ni gaba a koda yaushe.

“Tun jiya da na samu labarin za a rufe hanyoyi, aka kuma haramta taruka da jerin gwanon motoci a cikin gari na san cewa mu ne ake so a muzgunawa.

“Amma sai na faɗa wa kaina ai ba kakar siyasa ko yaƙin neman zaɓe ba ne yanzu.

“Don haka ni ba yaƙin neman zaɓe zan yi ba. Ni kaɗai ce zan shigo gari cikin mutane na, na yi shagalin bikin Sallah tare da su.

“Don haka babu wani laifi a ciki, babu dokar da na karya. A Najeriya muke. Ina da ’yancin shiga taruka da bukukuwa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Babban daraktan hukumar IAEA, Rafael Grossi, zai ziyarci Iran cikin makwanni masu zuwa
  • HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar Galadiman Kano
  • Basakkwacen da ya yi ridda ya sake karɓar addinin Musulunci
  • Iran Ta Bukaci Hukumar IAEA Ta Bayyana Matsayinta A Shirin Makamashin Nukliya Na Kasar
  • Duk Da Hanin Gwamna Da ‘Yansanda, Natasha Ta Isa Gida Kuma Ta Yi Taro
  • Babu dokar da na karya saboda yin taro a mazaɓata — Natasha
  • Sarki Sanusi Ya Yabawa Gwamna Yusuf Kan Manufofin Habaka Jama’ar Kano
  • Muna kiran Natasha ta jingine gangamin da za ta yi a Kogi — ’Yan sanda
  • Gwamna Edo Okpebholor Ya Jajantawa Iyalan Wadanda Aka Kashe
  • Kisan Mafarauta: Matakan da gwamnatin Edo da ta Kano suke ɗauka