Jirage su yi karo a sararin samaniya a Amurka
Published: 30th, January 2025 GMT
An zaƙulo gawarwakin mutane 19 bayan wani jirgin fararen hula da jirgin sojoji sun yi karo a sararin samaniya a ƙasar Amurka.
A cikin daren Laraba ne wani jirgin Kamfanin American Airlines dauke da fasinjoji 60 da ma’aikata hudu ya yi karo da wani helikwaftan sojojin Amurka, ƙirar Black Hawk, mai ɗauke da mutane a birnin Washington DC.
Jiragen da suka yi karo sun auka a cikin kogin Potomac, inda a halin yanzu ake aikin ceto, tun baya aukuwar hatsarin jiragen daga misalin ƙarfe 9 na dare.
Jami’an gwamnati sun tabbatar da cewa jirgin fasinjan na dauke da iyalai da kuma tawagar ’yan wasa Skating, bayan sun kammala atisaye.
DR Congo: Sojoji sun ƙaddamar da gagarumin hari kan ’yan tawayen M23 —Shugaba Tshisekedi Kungiyar NLC ta kira zanga-zanga kan ƙarin kuɗin wayaKafar yaɗa labaran ƙasar Rasha ta ce ’yan wasan Skating Dan ƙasar ma’aurata, Evgenia Shishkova da Vadim Naumov, suna cikin jirgin.
Ma’auratan sun lashe Gasar Skating na Duniya da aka gudanar a Amurka a shekarar 1994.
Sakataren Tsaron Amurka, Pete Hegseth, ya ce rundunar tsaron kasar ta fara bincike kan hatsarin jiragen, a yayin da Shugaba Donald Trump ya bayyana cewa hatsarin mummunan abu ne kuma da za a iya kauce wa.
Shugaban Hukumar Kashe Gobara na Birnin Washington DC, John A Donnelly Sr, ya ce aikin ceton yana da matukar sarkakiya, a yayin da aka dakatar da suka da tashin jirage zuwa ƙarfe 4 na yamma agogon GMT.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna ya dakatar da basarake kan satar mutane da yankinsa
Gwamnan Jihar Edo, Monday Okpebholo, ya dakatar da basaraken yankin Masarautar Uwano Kingdom, Dakta George Oshiapi Egabor, nan take saboda matsalar yi garkuwa da mutane a yankin.
Dakta George Oshiapi Egabor shi ne Okumagbe na Masarautar Uwano da ke Agenebode a Karamar Hukumar Etsako ta jihar.
Kakakin gwamnan, Fred Itua, a cikin wata sanarwa, ya bayyana cewa an dakatar da basaraken ne har sai abin da hali ya yi, saboda yawan samun kashe-kashe da kuma garkuwa da mutane a masarautarsa a baya-bayan nan.
Ya ce tuni jami’an tsaro suka tsare sakataren basaraken, Cif Peter Omiogbemhi, sakamakon wani sabon hari a da ya yi ajalin wani bafade, Cif John Ikhamate. Mutanen da aka kashe a Binuwai sun ƙaru zuwa 72 An tsinci gawar saurayi da buduwarsa a tuɓe a cikin daƙi A baya-bayan nan an samu yawaitar garkuwa da mutane a yankin, wanda ya haddasa ƙone ofishin ’yan sandan da ke kula da yankin. Daga cikin waɗanda aka yi garkuwa da su har da wasu malaman coci guda uku da aka yi aka yi awon gaba da su a wani coci, inda daga baya aka sako biyu bayan an biya kudin fansa, na ukun kuma aka kashe.