Aminiya:
2025-04-02@12:24:03 GMT

Hisbah ta kama masoya kan yin aure ba tare da amincewar iyayensu ba

Published: 30th, January 2025 GMT

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano, ta kama wani saurayi da budurwarsa bisa zargin yin aure a wajen wani taro ba tare da amincewar iyayensu ba.

A cewar Mataimakin Babban Kwamandan Hisbah, Sheikh Mujahid Aminudeen Abubakar, matasan sun yi auren ne a wajen shaƙatawa bayan wani da ba su da alaƙa da shi ya biya sadakin amaryar.

Meta zai biya Trump $25m kan rufe shafinsa Kungiyar NLC ta kira zanga-zanga kan ƙarin kuɗin waya

Ya bayyana cewa yin hakan ya saɓa wa ƙa’idar Musulunci kuma ba za a yarda da irin wannan lamarin ya ci gaba da faruwa a Kano ba.

“Muna sanar da cewa mun kama ma’auratan, kuma za mu ci gaba da bincike don kama abokansu da duk wanda ya taimaka wajen wannan auren na sirri domin hana irin wannan faruwa a gaba,” in ji shi.

Ya kuma yi kira ga jama’a da su kasance masu sanya ido kan irin waɗannan al’amura, tare da yaba wa waɗanda suka kai rahoton lamarin ga hukumar.

Ya ce tuni hukumar ta fara bincike kan lamarin domin sanin matakin da za ta ɗauka a kan ma’auratan.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Tsohon Gwamnan Zamfara Ya Bukaci A Ci Gaba Da Tallafawa Mabukata Bayan Ramadan.

Tsohon Gwamnan Jihar Zamfara kuma Sanata mai wakiltar mazabar Zamfara ta Yamma, Dakta Abdul’aziz Yari, ya yi kira ga ‘yan siyasa da masu hannu da shuni da su kara kaimi wajen gudanar da ayyukansu na alheri fiye da watan Ramadan.

 

Da yake zantawa da manema labarai a mahaifarsa Talatan Mafara, a wani bangare na sakonsa na Sallah, Yari ya jaddada muhimmancin ci gaba da al’adun bayar da Zakka, Sadaka, da sauran nau’o’in tallafi ga marasa galihu a duk shekara.

 

Ya yabawa gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa bullo da shirye-shiryen jin dadin jama’a da nufin inganta rayuwar ‘yan Najeriya.

 

Dokta Yari ya yi kira ga ‘yan kasar da su ba da cikakken goyon baya ga kokarin shugaban kasar na ciyar da kasar gaba.

 

“A madadin ‘ya’yan jam’iyyar APC na Zamfara da al’ummar mazaba ta, na mika sakon taya murna ga shugaba Tinubu na cika shekaru 73 da haihuwa. “Muna addu’ar Allah Madaukakin Sarki ya kara masa shekaru masu yawa cikin koshin lafiya, da wadata, da kuma hikimar da zai jagoranci kasar nan ta hanyar da ta dace. Za mu ci gaba da yi masa addu’ar samun nasara a matsayinsa na shugaban kasa,” inji shi.

 

 

COV/AMINU DALHATU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kisan Mafarauta: Babu wanda aka kai wa harin ramuwar gayya a Kano — Ƙungiyoyin Matasa
  • DG VON Yayi Kira Ga Zaman Lafiya Da Hadin Kai Don Fadada Ci gaban Tattalin Arziki Da Ci Gaba.
  • ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
  • Tsohon Gwamnan Zamfara Ya Bukaci A Ci Gaba Da Tallafawa Mabukata Bayan Ramadan.
  • Gwamnan Edo Ya Ziyarci Sanata Barau Kan Kisan Yan Arewa 16
  • Tsawa Ta Kashe Makiyayi Da Shanu A Kudancin Kaduna
  • Iran Ta Ce Tattaunawa Da Amurka Tare Da Mai Shiga Tsakani Na Gaba, Ya Danganci Matakan Da Ta Dauka Kan Iran
  • Ƴansanda Sun Kama Wanda Ya Kashe Ɗan Bijilanti A Tawagar Sarki Sunusi II
  • Ba Za A Iya Dakile Ci Gaban Hakkin Dan Adam Na Xizang Da Kowace Irin Karya Ba
  • Kashe Matafiya: Gwamnatin Kano Ta Aika Tawaga Zuwa Edo