Isra’ila ta dakatar da sakin fursunonin Palasɗinawa ba zato ba tsammani yayin da ake ci gaba da musayar fursunoni da waɗanda aka kama ƙarƙashin yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza, a cewar rahoton Army Radio.

Hukumomi ba su bayyana dalilin dakatarwar ba, kuma babu tabbas kan lokacin da za a ci gaba da tsarin.

Wani Ɗan Pakistan Ya Kashe ‘Yarsa Kan Ɗora Bidiyon Kanta A TikTok Hisbah Ta Kama Matashi Da Matashiya Kan Yin Aure Saɓanin Dokokin Musulunci A Kano

Yarjejeniyar tsagaita wutar an ƙulla ta ne don bayar da damar musayar fursunonin da Hamas ke riƙe da su da kuma waɗanda ke tsare a Isra’ila.

Sai dai wannan matakin ba zato ba tsammani ya haifar da rashin tabbas kan ci gaba da yarjejeniyar.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Falasɗinawa Isra ila Musaya

এছাড়াও পড়ুন:

Gaza : Red Crescent ta yi watsi da rahoton Isra’ila kan kisan da aka yi wa jami’an agaji

Kungiyar agaji ta Red Crescent ta Falasdinu ta yi watsi da rahoton da sojin Isra’ila suka fitar kan kisan da aka yi wa sama da jami’an agajin gaggawa na Gaza a watan da ya gabata, wanda gwamnatin kasar ta ce an kashe ne ta bisa kuskure.

Kungiyar ta yi fatali da rahoton na Isra’ila da cewa ba shi da inganci kuma ba za a amince da shi ba, tana mai jaddada cewa yana cike da karairayi.

A wani rahoto da suka fitar ka abinda ya faru sojojin Isra’ila sun yi ikirarin cewa, an samu ” kura-kurai da yawa” a kisan da akayi wa jami’an agajin a Gaza, suna masu cewa za a kori wani kwamandan sojoji.

“Binciken ya nuna cewa an samu wasu matsaloli na rashin da’a na kwararru, da rashin bin umarni, da kuma gaza yin cikakken bayani kan lamarin,” in ji rundunar.

A ranar 23 ga Maris, ne aka harbe wasu ma’aikatan agaji na Falasdinawa 15 da masu aikin ceto a kusa da Rafah da ke kudancin Gaza.

Sojojin Isra’ila sun sake nanata cewa shida daga cikin likitocin Falasdinawa 15 da Isra’ila ta kashe, ‘yan kungiyar Hamas ne.

Kisan da akayi wa jami’an agajin gaggawa na falasdinu ya fuskanci tofin Allah-tsine daga kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa da dama.

Lamarin dai ya sake fiddo a fili irin ta’asar da Isra’ila ke aikatawa a zirin Gaza.

Da farko dai Isra’ila ta yi ikirarin cewa sun bude wuta ne, saboda yadda motocin suka nufo, a cikin dare, ba fitilu, kuma babu wata masaniya da sojinta suke da a kan zuwan motocin.

Amma kuma daga baya hukumar sojin ta ce, wannan bayani da ta bayar akwai kuskure, bayan da aka gano wani hoton bidiyo a wayar daya daga cikin ma’aikatan agajin da sojin Isra’ilar suka kashe a wannan hari, hoton da ke nuna motocin na tafiya da fitilu a kunne da kuma duk wata alama da za ta fayyace su waye.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnan Edo Ya Dakatar da Sarki Saboda Matsalar Tsaro A Yankinsa
  • Gwamna ya dakatar da basarake kan satar mutane da yankinsa
  • Putin ya rattaba hannu kan yarjejeniyar hadin gwiwa da Iran
  • Wasu Falasdinawa Sun Yi Shahada A Harin Sojojin Mamayar Isra’ila Kan Zirin Gaza
  • Gaza : Red Crescent ta yi watsi da rahoton Isra’ila kan kisan da aka yi wa jami’an agaji
  • Bikin Easter : Paparoma Francis ya yi kira da a tsagaita wuta a Gaza
  • Sharhi:  Kalankuwar  Kona Rayayyu Da Wuta A Gaza
  • Hamas ta yi watsi da shirin kwance damara na Isra’ila
  • Kasar Rasha Ta Sanar Da Tsagaita Bude Wuta Da Ukraine Na Tsawon Kwanaki Bikin Ester
  • Tashin Gobara A Kwale-Kwale Ya Lashe Rayukan Mutane 143 A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango