Isra’ila ta dakatar da sakin fursunonin Palasɗinawa ba zato ba tsammani yayin da ake ci gaba da musayar fursunoni da waɗanda aka kama ƙarƙashin yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza, a cewar rahoton Army Radio.

Hukumomi ba su bayyana dalilin dakatarwar ba, kuma babu tabbas kan lokacin da za a ci gaba da tsarin.

Wani Ɗan Pakistan Ya Kashe ‘Yarsa Kan Ɗora Bidiyon Kanta A TikTok Hisbah Ta Kama Matashi Da Matashiya Kan Yin Aure Saɓanin Dokokin Musulunci A Kano

Yarjejeniyar tsagaita wutar an ƙulla ta ne don bayar da damar musayar fursunonin da Hamas ke riƙe da su da kuma waɗanda ke tsare a Isra’ila.

Sai dai wannan matakin ba zato ba tsammani ya haifar da rashin tabbas kan ci gaba da yarjejeniyar.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Falasɗinawa Isra ila Musaya

এছাড়াও পড়ুন:

HOTUNA: Abba da Gwamnan Edo sun ziyarci iyalan mafarautan da aka kashe a Edo

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf da takwaransa na Jihar Edo Monday Okpebholo, sun ziyarci garin Torankawa da ke Kano domin jajanta wa iyalai da yan uwan mafarautan nan guda 16 da aka kashe a Jihar Edo.

Gwamnonin biyu sun ziyarci garin ne da manufar tabbatar wa da iyalan waɗanda lamarin ya shafa cewa lallai gwamnatin jihar Edo za ta hukunta waɗanda suka yi wannan aika-aika sannan kuma gwamnatin za ta biya su diyya.

Ta zuba wa abokan aikinta guba bayan taƙaddama kan ƙarin matsayi Mene ne matsayin azumin Sitta Shawwal a Mazhabar Malikiyya

“Wannan ziyara ba kawai ta jaje da ta’aziyya ba ce, a’a ta nuna tabbacin ƙoƙarin samar da adalci.

“Iyalan waɗannan mamata na buƙatar abin da ya fi kalaman baka — suna buƙatar aiwatar da duk abin da aka faɗa za a yi musu.

“Ba za mu zauna ba har sai mun ga an kama waɗanda suka yi wannan aika-aika, sai an yi holinsu a bainar jama’a sannan a hukunta su,” in ji Abba Kabir.

A nasa ɓangaren gwamnan jihar ta Edo, Monday Okpebholo ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan inda ya ba su tabbacin cewa gwamnatinsa za ta yi adalci ba daɗewa ba.

Aminiya ta ruwaito cewa, Abba ya buƙaci Sanata Okpebholo da ya tabbatar da biyan diyyar mafarauta da aka kashe a jiharsa ta Edo a hanyarsu ta komawa gida domin bukuwan Sallah.

Abba ya bayyana haka ne a lokacin da Gwamna Monday ya jagoranci tawagar gwamnatinsa zuwa Kano domin jajanta wa gwamnati da al’ummar jihar bisa abin da ya faru na kisan matafiyan a makon jiya.

A jawabinsa, gwamna Abba ya yaba da ƙoƙarin takwaran nasa bisa matakan da ya ɗauka, inda ya ce a nasu ɓangaren sun ɗauki matakan da suka dace domin hana ramuwar gayya, “domin mutanen Kano masu son zaman lafiya ne da maraba da baƙi .

“Yawancin waɗanda aka kashe ɗin ’yan Kano ne. An tare su ne a jiharka a hanyarsu ta dawowa daga Fatakwal, aka gana musu azaba, sannan aka ƙone wasu daga cikinsu.”

Gwamna ya kuma yaba da ƙoƙarin gwamnatin Edo wajen ganin an ɗauko gawarwakin tare da binne su kamar addini ya tsara, da kuma kama wasu daga cikin waɗanda ake zargi.

Sai dai gwamna Abba Kabir Yusuf ya ce yana da buƙatu biyu da yake so gwamnan ya yi ƙoƙarin ganin an cika su.

A cewasa, “muna so a gabatar da waɗanda ake zargi a gaban menama labarai domin duniya ta gansu kowa ya ga fuskokinsu. Wannan zai taimaka wajen kwantar da hankalin iyalan waɗanda aka kashe,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa Gwamnan na Edo ya faɗa cewa masa za a tabbatar da hukunci, “kuma ina da tabbacin gwamna zai cika wannan alƙawarin.”

Ya ce, “abu na biyu shi ne muna so a tabbatar da biyan diyyar waɗanda aka kashe ɗin ga iyalansu. Na san kai mutum ne mai nagarta da cika magana, kamar yadda ka ce za a biya diyya, muna so a biya diyyar cikakkiya, kuma a cikin lokaci.”

Tun da farko, gwamna Monday Okpebholo ya bayyana takaicinsa kan yadda lamarin ya faru, inda ya ce tuni an kama mutum 14 da ake zargi suna da hannu a lamarin kuma za su tabbatar da sun fuskanci hukunci.

Bayan wannan ganawar ce da ta gudana a Fadar Gwamnatin Kano, Gwamna Abba ya jagoranci Gwamna Okpebholo zuwa garin Torankawa da ke Karamar Hukumar Bunkure, domin jajanta wa iyalan waɗanda aka kashe.

Okpebholo ya shaida wa iyalan cewa ba zai yi ƙasa a gwiwa ba har sai an tabbatar da adalci.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila na karbe yankuna a zirin Gaza
  • Uromi: Barau ya ziyarci iyalan waɗanda aka kashe, ya ba su kyautar N16m
  • Isra’ila ta kashe yara 322 cikin kwanaki 10 a Gaza — UNICEF
  • Sin Da Zambiya Sun Daddale Yarjejeniyar Fitar Da Kwarurun Macadamia Nuts
  • HOTUNA: Abba da Gwamnan Edo sun ziyarci iyalan mafarautan da aka kashe a Edo
  • Tsohon Gwamnan Zamfara Ya Bukaci A Ci Gaba Da Tallafawa Mabukata Bayan Ramadan.
  • HKI Ta Sake Kai Wa Unguwar Dhajiya Dake Beirut Hari
  • Muna so a nuna wa duniya mutanen da suka kashe ’yan Arewa a Edo — Gwamnan Kano
  • Gaza : Fiye da mutane 1,000 Isra’ila ta kashe tun daga ranar 18 ga Maris
  • Kisan Mafarauta: Matakan da gwamnatin Edo da ta Kano suke ɗauka