Aminiya:
2025-02-22@16:31:30 GMT

Mahaifi ya harbe ’yarsa har lahira saboda wallafa bidiyo a Tiktok

Published: 30th, January 2025 GMT

Hukumomi a birnin Quetta na Ƙasar Pakistan, sun kama wani mutum mai shekaru 50, kan zargin kashe ’yarsa mai shekaru 15 a duniya, saboda ta ƙi daina ɗora bidiyonta a kafar TikTok.

Rahoton ’yan sanda ya nuna cewar, mutumin ya dawo da iyalinsa daga Amurka zuwa Pakistan kwanan nan kafin aikata kisan.

Hisbah ta kama masoya kan yin aure ba tare da amincewar iyayensu ba Wata uku uami’o’i ba su da wutar lantarki —SSANU

Ya amsa laifin harbe ’yarsa, inda ya ce tana aikata abubuwan da ba su dace da addini da al’ada ba, ta hanyar saka bidiyo a TikTok.

An kuma kama ɗan uwansa kan zargin taimaka masa wajen aikata laifin.

Dukkaninsu sun nuna rashin amincewa da yadda matashiyar ke amfani da TikTok, wanda suka ce hakan ya saɓa wa tarbiyya mai kyau.

A halin yanzu, kotu ta bayar da umarnin tsare su na tsawon kwanaki 10 don ci gaba da bincike.

Irin wannan kisa ya zama ruwan dare a Pakistan, inda ’yan uwa ke kashe mata kan wani abu da suke ganin ya saɓa wa al’ada ko zai jawo wa danginsu abun kunya.

Wannan lamari ya tashi hankalin jama’a kan yadda ake amfani da kafofin sada zumunta da kuma tasirin al’adu a tsakanin iyalai.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda harbi

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Yi Tir Da Shugaban Hukumar IAEA Saboda Sanya Siyasa Da Daukan Bangare A Jawansa Na Baya Bayan Nan

Gwamnatin kasar Iran ta gargadi hukumar IAEA mai kula da al-amuran makamashin nukliya a duniya, bayan da babban sakataren kungiyar Rafaei Grossy ya fita daga matsayin dan ba ruwammu, a cikin harkokin siyasa a aikinsa, inda ya furta wasu jawabai dangane da shirin makamashin nukliya na kasar Iran.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Gorossi ya fita daga matsayinsa na gwararre da kuma masanin harkokin makamashin nukliya ya kuma dauki bangare a wani taro da yan jirudu da ya gabatar a birnin Tokyo na kasar Japan.

A cikin jawabin da yayi wa yan jaridu Grossi ya Iran tana ‘gasa makamashin Uranium har zuwa kasha 60% wanda ya kusan kaiwa ga makamashin Nukliya, sannan bata bawa hukumar IAEA hadin kai da yakamata.

Bayan wannan zancen na hukumar makamashin nukliya ta fitar da bayani inda take tuhumar Grossi da daukan bangare, kuma hukumarsa tana iya rasa iran ‘amincewar Iran’ da ayyukanta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ɗan Abacha ya kare mahaifinsa bayan ƙaddamar da littafin IBB
  • Sibil Difens ta cafke mutum 17 kan aikata sata a Yobe
  • Jirgin Saman Da Kasar Sin Ta Kera Mai Amfani Da Lantarki Ya Yi Tashin Farko Cikin Nasara
  • Gwamnatin Filato ta dakatar da haƙar ma’adinai saboda matsalar tsaro
  • ’Yan sanda sun daƙile satar mutane, sun kama wasu 3 a Borno
  • Amurka Ta Bawa HKI Makami Mai Karfi, MK-87
  • Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet
  • Iran Ta Yi Tir Da Shugaban Hukumar IAEA Saboda Sanya Siyasa Da Daukan Bangare A Jawansa Na Baya Bayan Nan
  • An rufe Jami’ar Kogi saboda zanga-zangar ɗalibai
  • Trump Na Amurka Ya Zargi Shugaban Kasar Ukiraniya Da Kama –Karya Da Kuma Rusa Kasarsa Ba Tare Da Wani Dalili Ba