Wani ya kashe ’yarsa saboda bidiyon TikTok a Pakistan
Published: 30th, January 2025 GMT
Wani uba a ƙasar Pakistan ya kashe ɗiyarsa matashiya bayan ta saka wasu faifan bidiyo da ya ɗauka a matsayin waɗanda ba su dace ba a manhajar sada zumunta ta TikTok, in ji ‘yan sanda a ranar Alhamis.
Shugaban ‘yan sandan yankin, Babar Baloch, ya ce mutumin wanda aka ce yana da shekara 50 a duniya, ya dawo da iyalansa daga ƙasar Amurka kwanan nan, domin su zauna a birnin Ƙuetta da ke Kudu maso Yammacin Pakistan.
Mahaifin, wanda yanzu haka yake tsare, ya amsa laifin harbe ’yarsa a farkon wannan makon bayan ta ƙi sanya suturar da ta dace kuma ta daina sanya bidiyon da ‘yan uwanta suka ɗauka a matsayin “bidiyon marasa mutunci” akan TikTok, in ji Baloch.
‘Yan sanda na ɗaukar lamarin a matsayin kisan gilla.
Kimanin mata 1,000 ne ake kashe wa a Pakistan ta hannun danginsu, uba, ’yan’uwa da ’ya’yansu bisa zargin ceto mutuncin iyali, a cewar Hukumar Kare Haƙƙoƙin Ɗan Adam ta Pakistan (HRCP).
Kungiyar kare haƙƙin bil adama ta Amnesty International ta ce waɗanda suka kashe a mafi yawan lokuta suna tserewa hukunci saboda wata doka ta Musulunci a cikin dokokin da ke bai wa ’yan uwan waɗanda aka kashe damar yafe wa wanda ya aikata laifin.
Pakistan ta amince da wata doka a shekara ta 2016 don kawar da wani ɓangare na magana mai cike da cece-kuce, amma hakan bai kai ga dakatar da wannan ɗabi’ar ba, a cewar HRCP.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
HOTUNA: Abba da Gwamnan Edo sun ziyarci iyalan mafarautan da aka kashe a Edo
Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf da takwaransa na Jihar Edo Monday Okpebholo, sun ziyarci garin Torankawa da ke Kano domin jajanta wa iyalai da yan uwan mafarautan nan guda 16 da aka kashe a Jihar Edo.
Gwamnonin biyu sun ziyarci garin ne da manufar tabbatar wa da iyalan waɗanda lamarin ya shafa cewa lallai gwamnatin jihar Edo za ta hukunta waɗanda suka yi wannan aika-aika sannan kuma gwamnatin za ta biya su diyya.
Ta zuba wa abokan aikinta guba bayan taƙaddama kan ƙarin matsayi Mene ne matsayin azumin Sitta Shawwal a Mazhabar Malikiyya“Wannan ziyara ba kawai ta jaje da ta’aziyya ba ce, a’a ta nuna tabbacin ƙoƙarin samar da adalci.
“Iyalan waɗannan mamata na buƙatar abin da ya fi kalaman baka — suna buƙatar aiwatar da duk abin da aka faɗa za a yi musu.
“Ba za mu zauna ba har sai mun ga an kama waɗanda suka yi wannan aika-aika, sai an yi holinsu a bainar jama’a sannan a hukunta su,” in ji Abba Kabir.
A nasa ɓangaren gwamnan jihar ta Edo, Monday Okpebholo ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan inda ya ba su tabbacin cewa gwamnatinsa za ta yi adalci ba daɗewa ba.
Aminiya ta ruwaito cewa, Abba ya buƙaci Sanata Okpebholo da ya tabbatar da biyan diyyar mafarauta da aka kashe a jiharsa ta Edo a hanyarsu ta komawa gida domin bukuwan Sallah.
Abba ya bayyana haka ne a lokacin da Gwamna Monday ya jagoranci tawagar gwamnatinsa zuwa Kano domin jajanta wa gwamnati da al’ummar jihar bisa abin da ya faru na kisan matafiyan a makon jiya.
A jawabinsa, gwamna Abba ya yaba da ƙoƙarin takwaran nasa bisa matakan da ya ɗauka, inda ya ce a nasu ɓangaren sun ɗauki matakan da suka dace domin hana ramuwar gayya, “domin mutanen Kano masu son zaman lafiya ne da maraba da baƙi .
“Yawancin waɗanda aka kashe ɗin ’yan Kano ne. An tare su ne a jiharka a hanyarsu ta dawowa daga Fatakwal, aka gana musu azaba, sannan aka ƙone wasu daga cikinsu.”
Gwamna ya kuma yaba da ƙoƙarin gwamnatin Edo wajen ganin an ɗauko gawarwakin tare da binne su kamar addini ya tsara, da kuma kama wasu daga cikin waɗanda ake zargi.
Sai dai gwamna Abba Kabir Yusuf ya ce yana da buƙatu biyu da yake so gwamnan ya yi ƙoƙarin ganin an cika su.
A cewasa, “muna so a gabatar da waɗanda ake zargi a gaban menama labarai domin duniya ta gansu kowa ya ga fuskokinsu. Wannan zai taimaka wajen kwantar da hankalin iyalan waɗanda aka kashe,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa Gwamnan na Edo ya faɗa cewa masa za a tabbatar da hukunci, “kuma ina da tabbacin gwamna zai cika wannan alƙawarin.”
Ya ce, “abu na biyu shi ne muna so a tabbatar da biyan diyyar waɗanda aka kashe ɗin ga iyalansu. Na san kai mutum ne mai nagarta da cika magana, kamar yadda ka ce za a biya diyya, muna so a biya diyyar cikakkiya, kuma a cikin lokaci.”
Tun da farko, gwamna Monday Okpebholo ya bayyana takaicinsa kan yadda lamarin ya faru, inda ya ce tuni an kama mutum 14 da ake zargi suna da hannu a lamarin kuma za su tabbatar da sun fuskanci hukunci.
Bayan wannan ganawar ce da ta gudana a Fadar Gwamnatin Kano, Gwamna Abba ya jagoranci Gwamna Okpebholo zuwa garin Torankawa da ke Karamar Hukumar Bunkure, domin jajanta wa iyalan waɗanda aka kashe.
Okpebholo ya shaida wa iyalan cewa ba zai yi ƙasa a gwiwa ba har sai an tabbatar da adalci.