Aminiya:
2025-03-03@10:51:04 GMT

An kashe mutumin da ya ƙone Al-Ƙur’ani a Sweden

Published: 30th, January 2025 GMT

An harbe mutumin da ya ƙone Al-Ƙur’ani, Salwan Momika, ɗan asalin ƙasar Iraƙi mai shekaru 38, a gidansa da ke Södertälje, kusa da birnin Stockholm a Sweden.

A harbe shi lokacin da yake ƙoƙarin wallafa bidiyo a kafar TikTok.

Sarkin yaƙin Zazzau ya rasu ana tsaka da taro  Hisbah ta kama masoya kan yin aure ba tare da amincewar iyayensu ba

Salwan Momika, ya ƙone Al-Ƙur’ani a 2023 a wajen Babban Masallacin Birnin Stockholm, lamarin da ya jawo cece-ku-ce da zanga-zanga a ƙasashen Musulmi.

Lamarin ya haifar da rikicin diflomasiyya, ciki har da kai hari ofishin jakadancin Sweden da ke Bagdad, da kuma korar jakadan Sweden da ke Iraƙi.

A halin yanzu, ’yan sanda sun kama mutum biyar da ake zargi da hannu a kisan, kuma suna ci gaba da bincike don gano musabbabin harin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Al Ƙurani Salwan Momika

এছাড়াও পড়ুন:

Hukuma ta kama ciyaman kan zargin badaƙalar filin N100m a Kano

Hukumar Karɓar Koke-Koke da Yaƙi da Cin Hanci ta Jihar Kano (PCACC), ta kama Shugaban Ƙaramar Hukumar Ƙiru, Abdullahi Mohammed, bisa zargin sayar da filin da aka tanada don gina Filin Wasa na Kafin Maiyaki.

Ana zargin cewa Mohammed, ya sayar wa wani kamfani mai suna Mahasum filin.

An ga watan Ramadan a Najeriya An ga jinjirin watan Ramadan a Saudiyya 

An gano cewar an tura kuɗin filin Naira miliyan 100 a asusun banki na shugaban.

Mai magana da yawun ƙaramar hukumar, Kabir Abba Kabir, ya tabbatar da kama Mohammed.

Ya tabbatar da cewa an tura jimillar kuɗi har Naira miliyan 240 tsakanin Nuwamba 2024 zuwa Fabrairu 2025, a asusunsa.

Sai dai hukumar ta ce ta karɓo kuɗaɗen haba ɗaya.

A cewar hukumar Mohammed, yana bayar da haɗin kai wajen binciken, yayin da hukumomi ke ƙoƙarin bankaɗo cikakkun bayanai game da badaƙalar.

Hukumar ta jaddada ƙudirinta na yaƙi da cin hanci da tabbatar da gaskiya a tafiyar da shugabanci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mu ne muka kai samame otal ba ’yan bindiga ba — EFCC
  • Hisba ta kama wasu matasa ba sa azumi a Kano
  • Fasinjoji 12 sun ƙone ƙurmus a hatsarin mota a Edo
  • Yan Ta’adda Sun kashe Sojojin Sa Kai Na Basij Biyu A Yankin Kudu Maso Gabacin Kasar Iran
  • An kama ɓarayin waya a Kano
  • Gobara ta ƙone sashen wani asibiti a Legas
  • Hukuma ta kama ciyaman kan zargin badaƙalar filin N100m a Kano
  • Sojoji sun kama shugaban ’yan bindiga, Kachallah Nabamamu a Zamfara
  • Sojoji sun kama shugaban ’yan bindiga, Kachallah Hassan Nabamamu a Zamfara
  • An kori ma’aikatan Microsoft saboda adawa da yahudawan sahyoniya