Aminiya:
2025-04-22@18:03:00 GMT

An kashe mutumin da ya ƙone Al-Ƙur’ani a Sweden

Published: 30th, January 2025 GMT

An harbe mutumin da ya ƙone Al-Ƙur’ani, Salwan Momika, ɗan asalin ƙasar Iraƙi mai shekaru 38, a gidansa da ke Södertälje, kusa da birnin Stockholm a Sweden.

A harbe shi lokacin da yake ƙoƙarin wallafa bidiyo a kafar TikTok.

Sarkin yaƙin Zazzau ya rasu ana tsaka da taro  Hisbah ta kama masoya kan yin aure ba tare da amincewar iyayensu ba

Salwan Momika, ya ƙone Al-Ƙur’ani a 2023 a wajen Babban Masallacin Birnin Stockholm, lamarin da ya jawo cece-ku-ce da zanga-zanga a ƙasashen Musulmi.

Lamarin ya haifar da rikicin diflomasiyya, ciki har da kai hari ofishin jakadancin Sweden da ke Bagdad, da kuma korar jakadan Sweden da ke Iraƙi.

A halin yanzu, ’yan sanda sun kama mutum biyar da ake zargi da hannu a kisan, kuma suna ci gaba da bincike don gano musabbabin harin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Al Ƙurani Salwan Momika

এছাড়াও পড়ুন:

NDLEA ta kama hodar iblis da aka ɓoye cikin littafai ana shirin kaiwa Saudiyya

Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi a Nijeriya NDLEA, ta yi nasarar kama hodar iblis wadda aka ɓoye a cikin littattafan addini da ake shirin kaiwa Saudiyya.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da Hukumar NDLEA ɗin ta fitar a ranar Lahadi.

Zaɓen 2027: Me ya sa jam’iyyu ke neman tabarrakin Buhari? Ruftawar gini ta kashe mutum 5 a Legas

Hukumar ta bayyana cewa ta kama ɗauri 20 na hodar iblis ɗin wanda jimillar nauyinsu ya kai giram 500 a cikin littattafan addini.

NDLEA ta ce jami’anta sun gano hodar ne a yayin da suke gudanar da bincike a wani kamfanin da ke jigilar kayayyaki a Legas a ranar Talata 15 ga Afrilun 2025, yayin da yake shirin kai kayayyakin zuwa Saudiyya.

Baya ga haka, hukumar ta NDLEA ta yi ƙarin bayani game da wasu jerin nasarori da ta samu a makon da ya gabata a ƙoƙarin da take yi na daƙile fataucin miyagun ƙwayoyi.

A wani kamfanin na daban da ke jigilar kayayyaki, hukumar ta NDLEA ta ce ta kama kilo 2.8 na tabar wiwin Loud wadda aka shigar da ita ƙasar daga Amurka.

A Kano, jami’an NDLEA sun kama wani matashi ɗan shekara 22 da haihuwa da ke sayar wa ‘yan fashi da haramtattun kayayyaki a lokacin da suke sintiri a hanyar Bichi zuwa Kano.

An kama matashin ne a ranar Lahadi, 13 ga watan Afrilun, yayin da yake kan hanyarsa ta zuwa Katsina ɗauke da kwalabe 277 na allurar pentazocine a ɗaure a cinyarsa da kuma cikin al’aurarsa.

Haka kuma, an kama wani da ake zargi mai suna Mohammed Abdulrahman Abdulaziz, mai shekaru 43, a ranar Lahadin da ta gabata a unguwar Rimin Kebe da ke Nasarawa a Kano tare da sunƙin wiwi nau’in skunk 68, wanda nauyinta ya kai kilo 30.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Tare Da Kwato Makamai A Kano
  • Hargitsi A Filin Wasan Kwallon Kafa Tsakanin Al-Ahly Tripoli Da Al-Suwaihli A Kasar Libiya
  • Hisbah ta kama tsohuwa kan zargin lalata da almajiri a Bauchi
  • Miji ya yi wa matarsa saki 3 a ofishin ’yan sanda
  • Gobara ta ƙone gidaje sama da 100 a sansanin ’yan gudun hijira a Borno 
  • NDLEA Ta Kama Masu Sayar Da Kwaya Ga Ƴan Bindiga A Kano
  • NDLEA ta kama hodar iblis da aka ɓoye cikin littafai ana shirin kaiwa Saudiyya
  • Faransa : An kama wata ‘yar Iran mai goyon bayan Falasdinu
  • Tawagar Gwamnati Ta Kai Ziyara Filato, Ta Sha Alwashin Kawo Karshen Kashe-kashe A Jihar
  • Muna Ganin Kashe-kashe Ta Ko’ina – ‘Yan Gudun Hijirar Sudan