Aminiya:
2025-03-03@09:45:56 GMT

Ana biyan wasu kuɗi don kare gwamnatin Tinubu — El-Rufai

Published: 30th, January 2025 GMT

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya yi zargin cewar akwai wasu shafaffu da mai da ake biya maƙudan kuɗaɗe domin kare Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.

Ya bayyana haka ne, yayin mayar wa Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa kan Harkokin Siyasar, Daniel Bwala, martani kan sukar da ya masa game da APC.

An kashe mutumin da ya ƙone Al-Ƙur’ani a Sweden Mahaifi ya harbe ’yarsa har lahira saboda wallafa bidiyo a Tiktok

El-Rufai ya yi wannan magana ne a wani taro da aka shirya kan ƙarfafa dimokuraɗiyya a Najeriya.

Tsohon gwamnan ya soki jam’iyyar APC saboda rashin kwatanta dimokuraɗiyya, inda ya ce bai gane inda jam’iyyar ta dosa a yanzu ba.

A yayin martaninsa ga El-Rufai, Bwala ya tambayi ko El-Rufai zai ci gaba da yin irin waɗannan kalamai idan yana cikin gwamnati.

Bwala ya ce: “Ɗan uwana, idan kana cikinagwamnati da majalisar zartarwa, shin za ka riƙa irin waɗannan kalamai? Tarihi yana cike da misalai.

“Gwamnatin da ka taka rawa aka kafa, yanzu ita kake son saukewa. Haba Mallam, a ji tsoron Allah mana.”

El-Rufai ya mayar da martani, inda ya ce: “Na yi minista shekaru 22 da suka wuce kuma Asiwaju ya fahimci cewa bana sha’awar kowane muƙami a cikin gwamnatinsa.”

Ya ƙara da cewa, “Idan na zauna a cikin gwamnatin Tinubu, zan ci gaba yin abin da nake ganin ba daidai ba ne.”

El-Rufai ya kuma soki wasu daga cikin mutanen da ya ke ganin ’yan siyasa ne da ake biya don kare gwamnatin Tinubu.

Ya ce, “Wannan wasa ne na siyasa da ake biyan wasu kuɗaɗe masu yawa don suke shiga shafukan sada zumunta don kare duk abin da gwamnatin Asiwaju.”

Ya kammala da cewa, “Ka more muƙamin mai bayar da shawara na musamman, ɗan uwana, amma ka tuna cewa biyayya ga Allah da ƙasa yana da muhimmanci sama da kowane mutum ko hukuma.”

Majalisar Dattawa ga ƙi amincewa El-Rufai ya zama minista a 2023, saboda ƙarar da wasu abokan hamayyarsa suka shigar a kansa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Bwala gwamnatin tinubu Siyasa tsohon gwamna El Rufai ya

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar Kare Hakkin Bil’adama ta ‘Euro-Med Monitor’ Ta Ce Ta Sami Shaidu Wadanda Suka Tabbatar Da Cewa HKI Tana Azabtar Da Fulasdinwa

Wata kungiyar kare hakkin bil’adama mai zaman kanta wacce take da cibiya a birnin Geneva na kasar Swizlanta ta bada sanarwan cewa ta sami cikekken shaidu wadanda suke tabbatar da cewa gwamnatin HKI tana azabtar da falasdinawa wadanda take tsare da su.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kungiyar tana bada wannan sanarwan a jiya Alhamis, ta kuma kara da cewa Jami’an gidajen yari da kuma sojjin HKI suna dukan kawo wuka kan falasdinawa da suka shiga hannunsu, sannan suna azabtar da su sosai, daga ciki har tare da yanke yanke wasu gabban jikinsu.

Kungiyar ta kara da cewa, mutum yana iya ganin alamun duka da kuma kumburan wurare da dama a jikin Falasdiwa.

Banda haka Falasdinawan da aka saka, sun bayyana cewa bayan duka da kuma azabtarwa sojojin HKI sukan hana magunguna ga wadanda basa da lafiya har wasunsu su rasa rayukansu.

Rahoton ya kara da cewa wadannan shaidun sun tabbatar da cewa, HKI tana aikata laifukan yaki, a kan al-ummar Falasdinu sannan alamu sun nuna cewa Falasdinawa da dama sun rasa rayukansu a gidajen yari k kuma wauraren da yahudawan suke tsare da su. Sannan HKI tana buye duk wata shaida da suke tabbatar da irin mummunar mu’amalan da suke yi da Falasdinawa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAJERIYA A YAU: Yadda za ku yi girke-girken azumi da kuɗi kaɗan
  • HKI Ta Yi Barazanar Shiga Rikicin Da Ya Barke  A Garin Jarmana Na Kasar Syria
  • Ramadan: ’Yan sanda sun tsaurara tsaro saboda azumi a Borno
  • Gobara ta ƙone sashen wani asibiti a Legas
  • Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet
  • Kwararrun Masana Sun Gargadi Kan Karkatar da Kudaden Fansho Na Biliyan ₦ 758
  • Tinubu ya sanya hannu a kasafin kuɗi na N54.99trn
  • Kungiyar Kare Hakkin Bil’adama ta ‘Euro-Med Monitor’ Ta Ce Ta Sami Shaidu Wadanda Suka Tabbatar Da Cewa HKI Tana Azabtar Da Fulasdinwa
  • Ka Cire Sarkin Kano Bayero Daga Fadar Nasarawa – Gwamnatin Kano Ga Tinubu
  • Cibiyar bincike ta nemi a tabbatar da dokar kare haƙƙin mata a Arewa