Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
Published: 30th, January 2025 GMT
Shugaban Afrika ta Kudu Cyril Ramaphosa ya mika gaisuwar sabuwar shekara da fatan alheri ga kasar Sin yayin da ta shiga sabuwar shekarar gargajiya. Cikin sakonsa a jiya Laraba, Cyril Ramaphosa ya bayyana kwarin gwiwar shekarar Maciji za ta ci gaba da karfafa matsayin Sin na karfin samar da kyawawan abubuwa da hikima da wadata na bai daya ga duniya.
Shi ma a jiyan, shugaban Zambia Hakainde Hichilema, ya aikewa shugaban kasar Sin Xi Jinping gaisuwar sabuwar shekarar gargajiya ta kasar, yana mai fatan samun ci gaban kasashen da al’ummominsu.
Kotu Ta Bayar Da Belin Sowore Kan Naira Miliyan 10 Kafar CMG Ta Samu Nasarar Yayata Shirin Shagalin Murnar Bikin Bazara A Kasashen WajeA ranar Talata kuma, shugaban Angola Joao Lourenco ya mika gaisuwar sabuwar shekara ga gwamnati da al’ummar Sinawa, yana mai fatan karfafa dangatakar kasarsa da Sin.
Shi ma shugaban Maldives Mohamed Muizzu, ba a bar shi a baya ba, domin a jiya Laraba ya aikewa takwaransa Xi Jinping da al’ummar Sinawa gaisuwa da fatan alheri a sabuwar shekara. Ya kuma yi fatan sabuwar shekarar za ta kawowa al’ummar Sin wadata da koshin lafiya da farin ciki. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban kasar Guinea-Bissau a ya yi wata ganawa da shugaban kasar Rasha
Shugaban Rasha Vladimir Putin da Shugaban Guinea-Bissau Umaro Sissoco Embalo sun tattauna a fadar Kremlin, yayin da ‘yan adawar Guinea-Bissau suka sha alwashin gurgunta kasar gabanin zabe.
Shugaban kasar Rasha Vladimir Putin da shugaban kasar Guinea-Bissau Umaro Sissoco Embalo, sun yi shawarwari a fadar Kremlin, a wani sabon salo na yunkurin da Moscow ke yi na kulla huldar tattalin arziki da tsaro da kasashen yammacin da tsakiyar Afirka.
Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya habarta cewa, hamshakin attajirin nan na Rasha Oleg Deripaska ya halarci tattaunawar da shugabannin biyu suka yi.
Kafofin yada labarai sun ambato wani minista a Guinea-Bissau, ya ce, Kamfanin aluminium na Rasha Rusal yana sha’awar gina layin dogo da tashar jiragen ruwa a kasar, da kuma binciken ma’adanai na bauxite.”
A wani labarin kuma, ‘yan adawa a kasar Guinea-Bissau sun lashi takobin kawo cikas ga harkokin rayuwa a kasar dake yammacin Afirka a yau Alhamis, sakamakon takaddamar da ta kunno kai dangane da wa’adin mulkin shugaba Umaro Sissoco Embalo na shekaru biyar zai kare.
Shugabannin ‘yan adawa sun ce a cewar Reuters, wa’adin Embalo zai kare ranar Alhamis, yayin da kotun kolin shari’a a Guinea-Bissau ta yanke hukuncin cewa wa’adin ta ya kare a ranar 4 ga Satumba.