Kamfanin dillancin labaran BBC ya bayyana cewa mutane 64 ne suke cikin jirgin fasinja na kamfanin American Airline, sannan mutane 3 ne a cikin jirgin yaki mai saukar ungulu samfurin Black Hawk suka yi karo a birnin washinton a safiyar yau Alhamis.

Labarin ya kara da cewa, a halin yanzu sun tashi daga kubutar da wadanda suke da rai zuwa neman gawaki kawai, tunda ana ganin da wuya a sami wani da rai a cikin fasinjojin jirgin.

Ya zuwa yanzu dai an tsamo gawakin mutane 30, kuma suna ci gaba da aikin gano wasu karin gawakin.

Jami’an gwamnatin kasar Amurka sun bayyana cewa jirgin fasinjar ya rabu zuwa kasha ukku sannan ya fada cikin wani ruwa mai zurfin mita 7.

Shugaba Trump dai ya bayyana cewa, hatsarin wanda za’a iya kauce wa ne, idan da kowa yayi aikin da ya dace. Don haka kuskuren dan’adama ne.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Zaɓen 2027: Babu ɗan takarar da zai yi nasara ba tare da goyon bayan Arewa ba — Hakeem

Tsohon mashawarcin Shugaba Bola Tinubu kan harkokin siyasa, Dokta Hakeem Baba-Ahmed, ya bayyana cewa babu wani ɗan siyasa da zai iya lashe kujerar shugabancin Nijeriya a Zaɓen 2027 ba tare da goyon bayan yankin Arewacin ƙasar ba.

Hakeem Baba-Ahmed ya bayyana hakan a wata hira ta bidiyo tare da tsohon Babban Sakataren Hukumar Kula da Inshorar Lafiya (NHIS), Farfesa Usman Yusuf.

NDLEA ta kama hodar iblis da aka ɓoye cikin littafai ana shirin kaiwa Saudiyya Zaɓen 2027: Me ya sa jam’iyyu ke neman tabarrakin Buhari?

Ya bayyana cewa nan ba da jimawa ba yankin Arewacin Nijeriya zai fuskanci alƙiblarsa ta siyasa.

“Nan da watanni shida mutanen Arewacin Nijeriya za su fayyace inda suka dosa, saboda haka zaɓi ya rage wa mutanen sauran yankunan ƙasar.

“Sai dai abin da muka sani ƙarara shi ne babu wanda zai zama shugaban Nijeriya ba tare da goyon bayan Arewa ba.

Ya bayyana damuwa kan yanayin da aka tsinci kai a ƙasar a halin yanzu, inda ya buƙaci ’yan Arewa da su guji faɗa wa tarkon ’yan siyasa mayaudara a zaɓen da ke tafe.

“Muna so a samu gwamnatin da ta fahimci matsalolinmu kuma wadda za ta iya magance su.

“Bayan shekaru takwas da Buhari ya yi a karagar mulki mun ƙara buɗe ido. A yanzu wata gwamnatin ce amma har yanzu kuka muke yi. Shikenan kullum a kuka za mu ƙare?

Kazalika, Baba-Ahmed ya bayyana yadda yankin Arewa ya tagayyara a sakamakon rikicin Boko Haram wanda ya taɓa duk mabiya addinai, lamarin da ya jaddada muhimmancin haɗin kai.

“Mun dawo daga rakiyar yaudarar da ake yi mana ta zaɓen ɗan takara saboda ƙabilanci ko addini. Yanzu an rufe wannan babi.

“Yanzu abin da kawai muke buƙata shi ne shugaba nagari wanda zai magance matsalolin da muke fama da su,” in ji shi.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Tare Da Kwato Makamai A Kano
  • Gwamna ya dakatar da basarake kan satar mutane da yankinsa
  • Ambaliyar Ruwa Ta Kashe Mutane 3, Ta Wanke Gonakin Shinkafa Sama Da Hekta 10,000 A Neja
  • An Yi Mummunar Arangama Da ‘Yan Bindiga A Sakkwoto
  • Sharhi:  Kalankuwar  Kona Rayayyu Da Wuta A Gaza
  • Zaɓen 2027: Babu ɗan takarar da zai yi nasara ba tare da goyon bayan Arewa ba — Hakeem
  • NDLEA ta kama hodar iblis da aka ɓoye cikin littafai ana shirin kaiwa Saudiyya
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Yaba Da Zaman Tattaunawan Iran Da Amurka Zagaye Na Biyu A Birnin Roma
  • Tashin Gobara A Kwale-Kwale Ya Lashe Rayukan Mutane 143 A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango
  • KOFIN DUNIYA: Za A Kara Yawan Kasashen Da Suke Bugawa Zuwa 64 A Shekarar 2030