Kafafen yada labarai na kasar Sweden sun bayyana cewa an sami gawar Selwan Momika dan shekara 38 a duniya a wani gida daga kudancin birnin Stokhom na kasar.

Selwan dai dan asalin kasar Iraki ne, wadanda yake gudun hijira a kasar ta Sweden tun, amma ya bayyana kansa a kafafen watsa labarai a shekara ta 2023 inda yake kona alkur’ani mai girma don wulakanta shi.

Saboda kuma nuna kiyayyarsa ga addinin musulunci da musulmi.

Gwamnatin kasar Sweden dai ta halattawa Selwan yin haka a karkashin dokar yencin fadin albarkacin baki wanda kasashen yamma musamman a turai suka amince da ita. Sai dai wannan aikin nasa ya gamu da fushin musulmi a duk fadin duniya.

Yansan da a birnin Stokhom sun tabbatar da c ewa sun ji karar bindiga a kudancin birnin a daren laraba, amma a lokacinda suka isa wurin sai suka sami wani mutum da harbin birnin. Amma bai dade bay a mutu.

Mai sharia Goran Lundahl na birnin ya tabbatar da cewa gawar ta Sewan ne amma har yanzun basu da masaniya kan yadda aka kashe shi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Araghchi : Iran a shirye take don tattaunawa amma barazanar soji daga Amurka na dagula yanayin’

Ministan harkokin wajen kasar Abbas Araghchi ya nanata shirin Tehran na shiga tattaunawar da Amurka kan shirinta na nukiliya na zaman lafiya, yana mai gargadin cewa barazanar soji daga Amurka na dagula halin da ake ciki a yanzu.

“Jamhuriyar Musulunci, kamar yadda ta kasance a baya, a shirye take don yin shawarwari na hakika,” in ji Araghchi a wata wayar tarho da takwaransa na Holland, Caspar Veldkamp, yau Laraba.

Ya jaddada cewa wannan “yana bukatar yanayi mai kyau da kuma nisantar hanyoyin da suka shafi barazana.”

Ministan ya yi Allah wadai da barazanar da jami’an Amurka suka yi wa Iran da cewa “ba za a amince da su ba”, ya kara da cewa sun saba wa kundin tsarin mulkin MDD da dokokin kasa da kasa, hasali ma suna “rikitar” halin da ake ciki.

Araghchi ya yi gargadin cewa Iran za ta mayar da martani “cikin gaggwa” ga duk wani cin zarafi a kan iyakokinta, huruminta, da kuma muradun kasarta.

A halin da ake ciki kuma, ya soki kungiyar Tarayyar Turai kan gazawarta na daukar matsaya kan kalaman na jami’an Amurka, wadanda ya ce suna barazana ga zaman lafiya da tsaron kasa da kasa.

A nasa bangaren, Veldkamp ya bayyana damuwarsa game da karuwar tashe-tashen hankula a yankin, yana mai jaddada bukatar hanyoyin diflomasiyya wajen warware takaddamar.

Shugaban Amurka Donald Trump ya yi barazanar a karshen mako cewa zai iya ba da umarnin kai hare-haren soji kan Iran idan Tehran ta ki shiga tattaunawa don “saka sabuwar yarjejeniya” kan shirinta na nukiliya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araghchi : Iran a shirye take don tattaunawa amma barazanar soji daga Amurka na dagula yanayin’
  • Kasar Sin Za Ta Yi Ramuwar Gayya Kan Takunkumin Biza Da Amurka Ta Kakaba Wa Jami’anta
  • Ma’aikatan Kasar Sin Sun Ceto Mutum 8 Zuwa Yanzu A Myanmar
  • Kasar Sin Mai Tabbatar Da Daidaito A Duniya Mai Cike Da Rashin Tabbas
  • Sanusi II Ya Gudanar Da Hawan Nassarawa Duk Da Umarnin ‘Yansanda A Kano
  • Gwamna Abba Ya Nemi A Bayyana Fuskokin Waɗanda Suka Kashe ‘Yan Arewa A Edo
  • Ana Share Fagen Gudanar Bikin Baje Kolin Kayayyakin Da Ake Shigar Da Su Kasar Sin Yadda Ya Kamata
  • An Fara Yakin Neman Zabe A Kasar Gabon
  • Iran Ta Zama Zakara A Wasan Kwallon Kafa Ta Bakin Teku Karo Na 4 Asiya
  • Jiragen Yakin Amurka Sun Kai Sabbin Hare-Hare Kan Kasar Yemen A Daren Jiya