Tsohon Shugaban Google: Deepseek Ya Kawo Muhimmin Sauyi A Bangaren AI
Published: 30th, January 2025 GMT
Tsohon shugaban kamfanin Google Eric Schmidt, ya bayyana bullar kamfanin DeepSeek na Sin a matsayin wadda ta kawo muhimmin sauyi ga takara a fagen kirkirarriyar basira ta AI a duniya.
Wannan na kunshe ne cikin wani sharhi da jaridar Washington ta wallafa ranar Talata, inda Eric Schmidt ya jaddada cewa, karfin Sin na yin takara da manyan kamfanonin fasaha ba tare da amfani da albarkatu mai yawa ba, ya nuna bukatar da Amurka ke da ita ta karfafa karfinta a bangaren.
DeepSeek kamfanin Sin ne dake mayar da hankali kan kirkirarriyar basira ta AI, wanda aka kafa a shekarar 2023. A cikin wannan watan na Junairun, kamfanin ya fitar da sabon samfurin AI mai suna DeepSeek-R1, wanda ya ja hankali sosai saboda kaifin basirarta. Aikin wannan sabon samfurin AI ya kai matsayin takara da tsare-tsaren AI kamar su ChatGPT na OpenAI, kuma an samar da shi ne kan farashi mai rahusa da bai kai na abokan takararsa ba.
Kaddamar da DeepSeek-R1 ya girgiza masa’antar fasahar zamani, lamarin da ya haifar da saukar farashin hannayen jari manyan kamfanonin fasaha kamar Microsoft da Meta da Nvidia. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha
এছাড়াও পড়ুন:
Matata ta taɓa kawo min ƙarar Akpabio — Mijin Natasha
Mijin Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, Emmanuel Oritsejolomi Uduaghan, ya bayyana cewa matarsa ta taɓa kawo masa ƙorafi game da cin zarafin da ta ce Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya yi mata.
A cewarsa, rikicin ya fara tun lokacin da Natasha ta tsaya takarar kujerar Sanata a 2019 a ƙarƙashin jam’iyyar SDP, inda ta nemi kujerar Sanatan Kogi ta Tsakiya.
Mu ne muka kai samame otal ba ’yan bindiga ba — EFCC Hisba ta kama wasu matasa ba sa azumi a KanoA lokacin, Akpabio yana riƙe da mukamin Ministan Neja Delta.
“Da kaina na je na same shi na buƙaci ya bai wa matata girman da ta cancanta, sannan ya girmama abotar da ke tsakaninmu.
“Bayan mun tattauna sai muka amince da a warware maganar cikin mutunci,” in ji shi.
Bayan zaɓen 2019, Natasha ta sake tsayawa takarar Sanata a 2023 a ƙarƙashin jam’iyyar PDP, inda ta samu nasara.
A lokacin, ana raɗe-raɗin cewa Akpabio bai ji daɗin yadda ta samu goyon baya ba, kuma hakan ya ƙara haddasa rashin jituwa a tsakaninsu.
“Amma bayan maganar da muka yi, sai matata ta ci gaba da bayyana damuwa game da irin cin zarafin da ta ke fuskanta daga shugaban majalisar.
“Ni dai na yarda da matata, kuma aure muka yi na soyayya da ƙauna. Babu abin da ya fi min ita a yanzu domin ita ce farin cikina.”
Natasha dai ta ce tana da wasu hujojji da za ta fitar, wanda ke nuna yadda Akpabio ya neme ta, lamarin da yanzu haka ya haifar da zazzafar muhawara a Najeriya.