KAROTA za ta kashe N250m wajen gyaran motoci 5 a Kano
Published: 30th, January 2025 GMT
Hukumar Kula da Hanyoyi da Sufuri ta Jihar Kano (KAROTA), ta ware Naira miliyan 250 domin gyaran wasu motocin aiki guda biyar.
Haka kuma, hukumar ta kashe Naira miliyan 250 domin sayen sabbin motoci domin amfanin da su.
Ana biyan wasu kuɗi don kare gwamnatin Tinubu — El-Rufai An kashe mutumin da ya ƙone Al-Ƙur’ani a SwedenKwamishinan Tsare-Tsare da Kasafin Kuɗi na Jihar, Musa Sulaiman Shanono ne, ya bayyana hakan yayin da yake bayani kan kasafin kuɗin shekarar 2025 da aka amince da shi.
Ya bayyana cewa ingantaccen tsarin sufuri yana da matuƙar muhimmanci ga bunƙasa tattalin arziƙi da ci gaban al’umma.
Ya kuma ce gwamnatin jihar na ƙoƙarin inganta kayan sufuri domin sauƙaƙa zirga-zirgar jama’a da kayayyaki a faɗin jihar.
“Tsarin sufuri yana da matuƙar muhimmanci ga ci gaban ƙasa da bunƙasar tattalin arziƙi. Don haka, gwamnatin jiha tana ɗaukar matakan da suka dace don inganta kayayyakin sufuri domin sauƙaƙa zirga-zirgar mutane da kayayyaki a ciki da wajen jihar,” in ji shi.
Shanono ya ƙara da cewa gwamnatin jihar ta ware Naira biliyan 13.32 don aiwatar da wasu muhimman ayyuka a ɓangaren sufuri, ciki har da sayen sabbin motocin ofis da kuma gyaran motocin aiki na hukumar KAROTA.
Ya tabbatar da cewa Naira miliyan 250 za a yi amfani da su wajen sayen motocin ofis, yayin da sauran Naira miliyan 250 ɗin za a kashe su wajen gyaran wasu motocin aiki guda biyar.
Kwamishinan ya yi ƙarin haske kan yadda motocin da za a gyara za su laƙume kuɗaɗe daidai da kuɗaɗen sabbin motocin da za a siya.
“Waɗannan motocin aiki ne, kuma manyan motoci ne. Ba za a iya haɗa su da motocin ofis da shugaba ke amfani da su ba, domin suna da bambanci,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gyaran Motoci Kwamishina Naira miliyan 250
এছাড়াও পড়ুন:
Tsohon shugaban hukumar NYSC ya kuɓuta daga hannun ’yan bindiga
Tsohon Shugaban Hukumar Kula da Matasa Masu Yi Wa Ƙasa Hidima (NYSC), Manjo Janar Maharazu Tsiga (mai ritaya), ya kuɓuta bayan shafe kwana 22 a hannun ’yan bindiga.
An sace shi ne a ranar 6 ga watan Fabrairu, 2025, a gidansa da ke garin Tsiga a Ƙaramar Hukumar Bakori a Jihar Katsina, yayin da wasu ’yan bindiga suka kai hari.
Ramadan: Saudiyya ta bai wa Kano da wasu jihohi kyautar dabino katan 1,250 Falalar Ramadan: Wata na rahama, gafara, da tsira daga wutaMaharan sun nemi kuɗin fansa Naira miliyan 250 kafin su sako shi.
Sai dai bayan tattaunawa, an biya kuɗin fansa, wanda ya kai ga sakinsa.
A halin yanzu, likitoci na kula da shi a wani asibiti da ba a bayyana ba sunansa ba.
A lokacin kai harin, sama da ’yan bindiga 100 ne suka afka gidansa, suka yi awon gaba da shi da wasu mazauna yankin.
Wasu mutum biyu sun samu raunuka yayin harin, yayin da wani daga cikin ’yan bindigar ya harbi ɗan uwansa bisa kuskure, wanda hakan ya yi sanadiyyar mutuwarsa.
Har yanzu, rundunar ’yan sandan Jihar Katsina ba ta fitar da wata sanarwa kan sakin tsohon shugaban NYSC ɗin ba.
Satar mutane da hare-haren ‘yan bindiga na ci gaba da zama babbar barazana ga tsaro a Jihar Katsina da sauran sassan Najeriya.
Gwamnatin Tarayya da hukumomin tsaro na fuskantar matsin lamba wajen shawo kan wannan matsala.