JMI Ta Cika Shekaru 46 Cib Da Nasarrar Juyin Juya Halin Mususlunci A Kasar, Wani Irin Ci gaba Ne Ta Samu A Cikin Wannan Lokacin
Published: 30th, January 2025 GMT
A ranar 11 Ga Watan Fabarainu na wannan shekarar ne JMI take cika shekaru 46 cib da samun nasara, da kuma kafa JM a Iran, wadanne nasarori ne kasar ta samu a cikin wannan lokaci?.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto kadan daga cikin nasarorin da kasar ta samu daga ciki.
01-Tsawon shekarun da Iraniyawa suke rayuwa ya karu daga 55 zuwa 76.
02-JMI ta iran ce kasa ta farko a duniya, a saurin ci gaba, a mafi yawan fannonin ilmi, wannan bisa rahoton manya-manyan cibiyoyin bincike da sanin hakan a duniya.
03-A bangaren ci gaban kayakin aikin likita, da kiwon lafiya, JMI ce ta farko a yankin gabas ta tsakiya sannan ita ce ta 17TH a duk duniya, shi ma bisa rahotannin cibiyoyin bincike da gano hakan a duniya.
04-JMI tana daga cikin kasashen duniya da suka sami ci gaban a zo a gani a bangarorin masu muhimmaci na aikin likita, wanda ake kira da turanci (stem cells) da kuma radio pharmaceuticals).
05-JMI ta shiga cikin kasashe 12 a duniya wadanda suke da dukkan abinda ake bukata na fasahar shiga cikin sararin samaniya. Sannan ta shiga cikin kasashe 5 a duniya wadanda suke da fasahar amfani da makamashin nukliya.
06-JMI ce kasa ta 13TH a fagen karfin soje, na 5 a fagen fasahar kera jiragen yaki wadanda ake sarrafasu daga nesa, sannan na 10 TH a fagen kera jirgen ruwa yaki mai tafiya karkashin ruwa, wato (subnerins ).
07-kungiyoyin wasanni motsa jiki mata kadai sun sami lambobin yabo kama daga zinari, azurka da tagulla har 7,961 a wasannin kasa da kasa. Sannan mata 335 ne suka zama alkalai a wasannin daban-daban a cikin shekara ta 2024 kadai.
Wannan kadannan Kenan daga irin ci gaban da JMI ta samu a cikin ci gaba a cikin al-amura daban daban a duniya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Wani Asbiti A Amurka Ya Kori Wata Likita Daga Aiki Bayan Ta Yi Allawadai Da Yahudawan Sahyoniyya
Asbitin ‘Mount Sinai’ (Dotsen Sinaa’ a kasar Amurka ta salami wata likita daga aiki, bayan da aika da wani rubutu da hoto a shafukan yanar gizo tana, wanda Asbitin tana cewa ai Musanta hare-haren ranar 7th ga watan Octoba ne’.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ta bayyana cewa Dr Leila Abbasi,diyar shekara 46 a duniya, ta aika sako cikin shafinta na yanar gizo inda take goyon bayan kungiyoyin Hamas da Hizbullah na kasar Lebanon sannan tana allawadai da kuma aibata HKI kan kissan yara da take yi a Gaza.
Gwamnatin kasar Amurka dai tana ganin kanta a matsayin kasa wacce take gaba wajen kare hakkin fadin albarkacin baki, amma idan al-amarin ya shafi HKI sai ta nuna fuska biyu. Ta kuma kareta ido a rufe kamar sauran Amurkawa da kuma kasashen duniya basa kallo.
Tun ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023 zuwa yanzu sojojin HKI ta kashe falasdinawa akalla dubu 50 a gaza kashi 2/3 daga cikinsu mata da yara ne.
Sannan abin ya yi muni inda gwamnatin Amurka ta tsaya gaban kotun ICC wacce ta tabbatar da laifukan HKI, ta kuma bada sammacin kama Firai ministan HKI da tsohon ministan yakin sa Yoav Galant. Inda ta kakabawa jami’an kotun takunkuman tattalin arziki.