A ranar 11 Ga Watan Fabarainu na wannan shekarar ne JMI take cika shekaru 46 cib da samun nasara, da kuma kafa JM a Iran, wadanne nasarori ne kasar ta samu a cikin wannan lokaci?.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto kadan daga cikin nasarorin da kasar ta samu daga ciki.

01-Tsawon shekarun da Iraniyawa suke rayuwa ya karu daga 55 zuwa 76.

2 , saboda ci gaban da kasar ta samu a bangaren kiwon lafiya. Wadanda suka hada da kayakin aiki magunguna da kwararrun likitoci da ma’aikatan jinya. Sannan wannan duk ya faru ne a cikin takunkuman kasashen yamma wadanda basa son ci gaban kasar, tun ranar kafuwarta har yau.

02-JMI ta iran ce kasa ta farko a duniya, a saurin ci gaba, a mafi yawan fannonin ilmi, wannan bisa rahoton manya-manyan cibiyoyin bincike da sanin hakan a duniya.

03-A bangaren ci gaban kayakin aikin likita, da kiwon lafiya,  JMI ce ta farko a yankin gabas ta tsakiya sannan ita ce ta 17TH  a duk duniya, shi ma bisa rahotannin cibiyoyin bincike da gano hakan a duniya.

04-JMI tana daga cikin kasashen duniya da suka sami ci gaban a zo a gani a bangarorin masu muhimmaci na aikin likita, wanda ake kira da turanci (stem cells) da kuma radio pharmaceuticals).

05-JMI ta shiga cikin kasashe 12 a duniya wadanda suke da dukkan abinda ake bukata na fasahar shiga cikin sararin samaniya. Sannan ta shiga cikin kasashe 5 a duniya wadanda suke da fasahar amfani da makamashin nukliya.

06-JMI ce kasa ta 13TH a fagen karfin soje, na 5 a fagen fasahar kera jiragen yaki wadanda ake sarrafasu daga nesa, sannan na 10 TH a fagen kera jirgen ruwa yaki mai tafiya karkashin ruwa, wato (subnerins ).

07-kungiyoyin wasanni motsa jiki mata kadai sun sami lambobin yabo kama daga zinari, azurka da tagulla har 7,961 a wasannin kasa da kasa. Sannan mata 335 ne suka zama alkalai a wasannin daban-daban a cikin shekara ta 2024 kadai.

Wannan kadannan Kenan daga irin ci gaban da JMI ta samu a cikin ci gaba a cikin al-amura daban daban a duniya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An ga jinjirin watan Ramadan a Saudiyya 

Hukumomi a Ƙasar Saudiyya, sun tabbatar da ganin jinjirin watan Ramadan da yammacin yau Juma’a.

Hakan na nuni da cewa azumin bana zai fara a ranar Asabar, 1 ga watan Maris, 2025.

Shafin Haramain Sharifain ne, ya tabbatar da wannan sanarwa, yayin da aka ga jinjirin watan a wurare daban-daban na ƙasar.

Sojoji sun kama shugaban ’yan bindiga, Kachallah Hassan Nabamamu a Zamfara Rage Albashi: Abba ya dakatar da muƙaddashin shugaban ma’aikatan Kano

Wannan na nufin cewa Musulmai a Saudiyya za su fara azumi a ranar Asabar.

Hakazalika, ƙasashen Qatar da Oman sun sanar da cewa za su fara azumin Ramadan a wannan ranar Asabar.

A yayin da ake shirin shiga wannan wata mai alfarma, an yi kira ga Musulmai da su yi amfani da lokacin azumi wajen ƙara yawan ibada, yin kyawawan ayyuka, da taimaka wa marasa galihu, duba da yanayin tattalin arziƙin duniya.

Ana sa ran cewa, Saudiyya da wasu ƙasashe, za a fara azumin Ramadan a sassa daban-daban na duniya a ranar Asabar, 1 ga watan Maris, 2025.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Yi Jana’izar Shugaban Kasar Namibia Da Ya Samo Mata ‘Yanci
  • Matata ta taɓa kawo min ƙarar Akpabio — Mijin Natasha
  • Babban Sakataren MDD Ya Taya Musulmi Murnar Shiga Watan Ramadan
  • An Samu Karuwar Jigilar Kayayyaki A Sabuwar Tashar Jigila Da Ta Hada Sin Da Kasashen Ketare
  • Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murna Fara Azumin Ramadan
  • Sakon Sakatare Janar Na Majalisar Dinkin Duniya Na Murna Fara Azumin Ramadan
  • Noman Rani: Tinubu Ya Amince Da Fadada Madatsun Ruwa 12 A Nijeriya
  • An ga jinjirin watan Ramadan a Saudiyya 
  • Bude Kasar Sin Na Kyautata Ci Gaban Duniya
  • Ɗabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta