A ranar 11 Ga Watan Fabarainu na wannan shekarar ne JMI take cika shekaru 46 cib da samun nasara, da kuma kafa JM a Iran, wadanne nasarori ne kasar ta samu a cikin wannan lokaci?.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto kadan daga cikin nasarorin da kasar ta samu daga ciki.

01-Tsawon shekarun da Iraniyawa suke rayuwa ya karu daga 55 zuwa 76.

2 , saboda ci gaban da kasar ta samu a bangaren kiwon lafiya. Wadanda suka hada da kayakin aiki magunguna da kwararrun likitoci da ma’aikatan jinya. Sannan wannan duk ya faru ne a cikin takunkuman kasashen yamma wadanda basa son ci gaban kasar, tun ranar kafuwarta har yau.

02-JMI ta iran ce kasa ta farko a duniya, a saurin ci gaba, a mafi yawan fannonin ilmi, wannan bisa rahoton manya-manyan cibiyoyin bincike da sanin hakan a duniya.

03-A bangaren ci gaban kayakin aikin likita, da kiwon lafiya,  JMI ce ta farko a yankin gabas ta tsakiya sannan ita ce ta 17TH  a duk duniya, shi ma bisa rahotannin cibiyoyin bincike da gano hakan a duniya.

04-JMI tana daga cikin kasashen duniya da suka sami ci gaban a zo a gani a bangarorin masu muhimmaci na aikin likita, wanda ake kira da turanci (stem cells) da kuma radio pharmaceuticals).

05-JMI ta shiga cikin kasashe 12 a duniya wadanda suke da dukkan abinda ake bukata na fasahar shiga cikin sararin samaniya. Sannan ta shiga cikin kasashe 5 a duniya wadanda suke da fasahar amfani da makamashin nukliya.

06-JMI ce kasa ta 13TH a fagen karfin soje, na 5 a fagen fasahar kera jiragen yaki wadanda ake sarrafasu daga nesa, sannan na 10 TH a fagen kera jirgen ruwa yaki mai tafiya karkashin ruwa, wato (subnerins ).

07-kungiyoyin wasanni motsa jiki mata kadai sun sami lambobin yabo kama daga zinari, azurka da tagulla har 7,961 a wasannin kasa da kasa. Sannan mata 335 ne suka zama alkalai a wasannin daban-daban a cikin shekara ta 2024 kadai.

Wannan kadannan Kenan daga irin ci gaban da JMI ta samu a cikin ci gaba a cikin al-amura daban daban a duniya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sahel: CILSS ta yi gargadi game da sake bullar ‘’kwarin dango’’ a yankin sahel

Kwamitin kasa da kasa kan yaki da fari a yankin Sahel (CILSS) ya yi wani gargadi na musamman kan sake bullar ‘’kwarin dango’’ a yankin Sahel, wanda ke da hadarin yin illa nan gaba.

Shafin yanar gizo na CILSS ya bayar da rahoton cewa, “Kwananan kwararru kan yaki da fari sun fitar da sanarwar sake bullar farar kwarin dango a kasashen Sahel da dama.”

CILSS ta yi gargadin cewa “, wannan na iya haddasa matsala sosai a lokacin noma a yankin da ya riga ya kasance mai rauni’’.

Yayin da ake fuskantar wannan barazana, CILSS na ganin cewa, ya zama wajibi a ba da goyon baya mai dorewa ga kasashendake sahun gaba wajen fuskantar irin wannan matsala na yankin Sahel, wajen aiwatar da shirye-shiryensu na gaggawa, domin dakile duk wata matsalar fari da ka iya yin illa ga kakar noma mai zuwa a yankin Sahel.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin: Amurka Ta Buga Harajin Fito Kan Sassa Daban Daban Ba Tare Da Nuna Sanin Ya Kamata Ba
  • Iran Zata Gudanar Da Tarin Kare Hakkin Bil’adama Ta Faskar Gabacin Duniya A Karo Na Farko
  • Illolin Da Manufar Haraji Kan Kayayyaki Ta Haifar A Kan Amerikawa
  • Gwamnan Edo Ya Dakatar da Sarki Saboda Matsalar Tsaro A Yankinsa
  • Sahel: CILSS ta yi gargadi game da sake bullar ‘’kwarin dango’’ a yankin sahel
  • Sharhin Bayan labarai: Rage Kasafin Kudin Ma’ailatar harkokin wajen Amurka da tasirinsa
  • Hisbah A Katsina Ta Musanta Zargin Cin Zarafin Wata Budurwa A Wani Faifan Bidiyo
  • Wasu Falasdinawa Sun Yi Shahada A Harin Sojojin Mamayar Isra’ila Kan Zirin Gaza
  • Gobara ta ƙone gidaje sama da 100 a sansanin ’yan gudun hijira a Borno 
  • Ruftawar gini ta kashe mutum 5 a Legas