Aminiya:
2025-03-03@09:34:59 GMT

Gwamnan Filato ya kori kwamishinoni 5

Published: 30th, January 2025 GMT

Gwamnan Jihar Filato, Caleb Mutfwang, ya kori kwamishinoni guda biyar daga muƙamansu.

Wannan ma cikin wata sanarwa da Sakataren Gwamnatin Jihar, Architect Samuel Jatau, ya fitar da yammacin ranar Alhamis.

Ɓarayin dabobbi sun shiga hannu, an ƙwato awaki 85 a Gombe Ana biyan wasu kuɗi don kare gwamnatin Tinubu — El-Rufai

Sanarwar ta bayyana cewa sauke kwamishinonin na daga cikin matakan da gwamnatin jihar ta ɗauka, sai dai ba a bayyana dalilin korarsu ba.

Sanarwar ta bayyana cewa korar kwamishinonin ba zai rasa nasaba da gudanar da aikinsu yadda ya kamata ba, musamman ganin yadda suka kwashe shekara guda wajen gudanar da ayyukansu.

A cewar wata majiya, gaza yin aiki yadda ya kamata ne ya sa aka cire su daga muƙamansu.

Kwamishinonin da aka sauke sun haɗa da: Chrysanthus Dawam, wanda ke riƙe da ma’aikatar kasafin ku6di da tsara tattalin arziƙi, Noel Nkup, wanda ke jagorantar ma’aikatar matasa da wasanni.

Ragowar sun haɗa da Jamila Tukur, Kwamishinar ma’aikatar yawon buɗe ido, Obed Goselle, wanda ke kula da ma’aikatar kimiyya da ƙere-ƙere, da Sule Musa, wanda ke jagorantar ma’aikatar ciniki da masana’antu.

Wannan mataki ya ɗauki hankalin al’umma, musamman mazauna jihar, inda ake ta hasashe kan yadda sauke kwamishinoni guda biyar zai shafi gudanar da ayyukan gwamnatin jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamna Calen Kwamishinoni

এছাড়াও পড়ুন:

GORON JUMA’A

Sako daga Alawiyya Jilani Jihar Kano:

Ina gaishe da Mummy da Abba, da kannena Zuhra, Sajida, Alhaji, da dukkanin kawayena na islamiyya dana boko wadanda muka kammala dukka, ina gaida Khadija (Sweet Bala), ina gaishe da Siyama Abdul, ina gaishe da Aunty Hajara da sauran ‘yan’uwa da fatan sakon ya iso gare ku kuma da fatan kun yi juma’a lafiya.

Sako daga Balaraba Ibrahim Jihar Kaduna:

Assalam.. Dan Allah a gaishe mun da Sisi ‘yar fucika uwar tsokana, da Hajiya Hazira, da Aunty Amina mai sakwara, ina gaishe da baby nice, da Binta kwaram da sauran wadanda ban gaisar ba wanda suka sanni.

Sako daga Yusuf Uba Muhammad Jihar Kano:

Haj. Rabi’at dan Allah a mikan sakon gaisuwata zuwa ga Baffa Salisu da abokaina kamar su; Zayyanu, Hassan, Fatuhu, Mansur, Aliyu dan ball, su Idris, Shafi’u dake garin Katsina, Alkhairin Allah ya kai masa, sannan ina gaishe da budurwata Maryam Baby, Allah ya sa ta yi juma’a lafiya.

Sako daga Bilyaminu Ahmad Jihar Kaduna:

Sakona zuwa ga dukkanin al’ummar musulmi ne na fadin duniya, ina gaishe da kowa kuma ina yi mana addu’ar fara azumi lafiya mu gama lafiya dan isar Annabi da alkur’ani.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda za ku yi rajista a shafin Itikafi a Saudiyya
  • Yadda ’yan bindiga suka sace ɗalibai 4 a Jami’ar Tarayya ta Dutsinma
  • Girke-girken Azumi: Yadda ake yin Tsiren Dankali
  • Sojoji sun kama shugaban ’yan bindiga, Kachallah Nabamamu a Zamfara
  • Sojoji sun kama shugaban ’yan bindiga, Kachallah Hassan Nabamamu a Zamfara
  • Ka Cire Sarkin Kano Bayero Daga Fadar Nasarawa – Gwamnatin Kano Ga Tinubu
  • Dalilin Dakatar Da Shugaban Ma’aikatan jihar Kano
  • An kori ma’aikatan Microsoft saboda adawa da yahudawan sahyoniya
  • Gwamnatin Kano Ta Shirya Taron Bita Don Jami’an Watsa Labarai
  • GORON JUMA’A