Dandalin sada zumunta na TikTok ya sanar da hada gwiwa da kamfanin tallace-tallace ta kafofin zamani na Aleph Holdings da dandalin sayayya kan intanet na kasar kenya wato Wowzi, wanda ake sa ran zai bunkasa tattalin arziki mai nasaba da kirkire-kirkiren jama’a a kasar Kenya.

Carl Jordon, shugaban sashen tallace tallace da harkokin cinikayya a yankin kudu da hamadar Sahara na kamfanin TikTok, ya shaidawa manema labarai a Nairobi cewa, hadin gwiwa da kamfanin Aleph holdings zai saukakawa harkokin kasuwanci a kasar wajen tallata kayayyaki da hidimominsu a kan dandalin wallafa bidiyo na wayar salula.

Ya ce hadin gwiwar ya nuna kudurin TikTok na karfafa muhallin kirkire-kirkire na jama’a a cikin gida ta hanyar tabbatar da masu basira sun samu kyakkyawan sakamako. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Shirin Tsaftar Muhalli Na Wata Wata Saboda Jarrabawar JAMB

A kokarinta na ganin an gudanar da jarrabawar hadin gwiwa ta hukumar shirya jarabawar shiga jami’a ta JAMB, gwamnatin jihar Kano ta dakatar da aikin tsaftar muhalli na watan Afrilun 2025.

 

An dauki wannan matakin ne bayan nazari da tuntubar masu ruwa da tsaki, a kokarin baiwa daliban jihar Kano damar rubuta jarabawarsu ba tare da wata matsala ba.

 

A wata sanarwa da Daraktan wayar da kan jama’a na ma’aikatar muhalli da sauyin yanayi, Ismail Garba Gwammaja ya fitar, ya ruwaito kwamishinan yana cewa.

 

“Dakatar na da nufin hana duk wani cikas da zai iya kawo cikas ga aikin jarrabawar da kuma tabbatar da cewa ‘yan dalibai za su iya zana jarabawarsu ba tare da wani shamaki ba, in ji Kwamishinan.

 

Kwamishinan Muhalli da Sauyin yanayi, Dr Dahiru M. Hashim, ya tabbatar wa mazauna jihar cewa dakatarwar na wucin gadi ne na wannan watan kawai, kuma za a ci gaba da aikin tsaftar mahalli ga baki daya a wata mai zuwa, Mayu 2025, a jihar.

 

Kwamishinan, ya yi kira ga mazauna yankin da su ba hukuma hadin kai da fahimtar dalilin da ya sa aka yanke wannan hukunci.

 

“Mun himmatu wajen tabbatar da tsafta da lafiya, kuma za mu yi aiki tukuru don ganin cewa ayyukan tsaftar muhalli ba su ci karo da wasu muhimman abubuwan da ke faruwa a jihar ba.”

 

Yayin da yake yabawa mazauna yankin bisa fahimtarsu da hadin kai da gwamnati mai ci, ya bukace su da su daina zubar da shara ba gaira ba dalili.

 

“kuma muna ba da hadin kai da ma’aikatan tsaftar muhalli don tabbatar da tsafta da lafiya a ko da yaushe, tare da yin addu’ar samun nasara ga daliban da za su zana jarabawar shiga jami’a ta JAMB ta hadin gwiwa.”

 

KHADIJAH ALIYU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Shirin Tsaftar Muhalli Na Wata Wata Saboda Jarrabawar JAMB
  • Uwargidan Shugaban Kasar Sin Ta Tattauna Da Takwararta Ta Kasar Kenya
  • Kare-Karen Haraji Ba Zai Bunkasa Arzikin Amurka Ba
  • Sin Da Kenya Sun Daukaka Dangantakarsu Yayin Da Xi Da Ruto Suka Gana
  • Shawarar Tabbatar Da Tsaro A Duniya Ta Samar Da “Kyakkyawan Fata” Ga Duniya Mai Fama Da Tashin Hankali
  • Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Aikin Inganta Hadin Gwiwar Jama’a Da Soja
  • IMF: Rashin Tabbas Zai Dagula Tattalin Arzikin Duniya
  • Sabbin Haraji: Yadda ‘Yan Bindiga Ke Tilasta Wa Jama’a Biyan Miliyoyin Kuɗi A Zamfara
  • Hajjin 2025: Sahun Farko Zai Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki 9 Ga Watan Mayu
  • Kungiyar BRICK Ta Rattaba Hannu A Kan Yarjeniyar Raya Ayyukan Noma A Duniya