Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-04-02@12:37:27 GMT

Kasar Sin Za Ta Zuba Jari A Karamar Hukumar Birnin Kudu

Published: 31st, January 2025 GMT

Kasar Sin Za Ta Zuba Jari A Karamar Hukumar Birnin Kudu

Karamar Hukumar Birnin kudu ta jihar Jigawa ta bada tabbacin hada kai da duk wata hukuma ko kamfani dake da muradin cigaban yankin.

Shugaban karamar hukumar, Dr. Muhammad Uba Builder ya bada wannan tabbacin lokacin da wakilan rukunin kamfanonin kasar Sin wato China suka ziyarce shi a ofishinsa.

Yace karamar hukumar Birnin kudu tana sahun gaba wajen zaman lafiya da karbar baki a fadin jihar.

Mista Sheng ya shaidawa shugaban karamar hukumar niyyar sa ta kafa kamfanin sarrafa takin zamani a yankin domin bunkasa aikin gona.

Yana mai cewar zai samar da kamfanin yin kujeru da gado da sauran kayayyaki domin bunkasa al’amuran kasuwanci a yankin.

Yace zai kuma samar da sinadarin da zai taimakawa manoma wajen samun amfanin gona mai yawa a lokutan noman rani har ma da na damina.

Wakilinmu ya bamu rahoton cewar, a fanin lafiya kuwa, a zancen da ake yi yanzu, hukumar kula da lafiya matakin farko ta karamar hukumar Birnin kudu da hukumar kula da lafiya ta majalisar dinkin duniya sun yabawa shugaban karamar hukumar bisa kokarinsa na tallafawa al’amuran rigakafi a yankin.

Manajan hukumar Alhaji Bello Abdulkarim wanda ya jagoranci tawagar hukumomin biyu zuwa ofishin shugaban karamar hukumar, ya danganta nasarorin da ake samu bisa hadin kai da goyon bayan shugaban wajen gudanar da ayyukan rigakafi a yankin.

Da yake mai da jawabi, shugaban karamar hukumar Alhaji Muhammad Uba Builder, ya bada tabbacin ci gaba da tallafawa harkokin kiwon lafiya bisa la’akkari da muhimmacin ta.

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Kasar Sin Zuba Jari shugaban karamar hukumar karamar hukumar Birnin

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Tinubu Ya Tube Kyara A Matsayin Shugaban Kamfanin NNPC Ya Kuma Sannan Ya Maye Gurbinsa

Shugaba Bola Ahmed Tinubu na tarayyar Najeriya ya tube shugaban kamfanin man fetur ta kasa NNPC Mele Kyari, da majalisar gudanarwansa, ya kuma maye gurbinsa ta

Jaridar Premium times ta Najeriya ta nakalto kakakin fadar shugaban kasa Bayo Onanuga a safiyar yau Asabar a shafinsa X.

Onanuga shugaba ya tube shugaban kamfanin na NNPC da majalisar gudanarwan sa wadanda aka nada su a cikin watan Nuwamban shekara ta 2023. Tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya nada Kyara a matsayin shugaban kamfanin sannan ya sake nada shi a shekara ta 2023.

Banda haka shugaba Tinubu ya nada Engineer Bashir Bayo Ojulari, a matsayin sabon shugaban kamfanin sannan da wasu yan majalisar gudanarwa 11. Sannan majalisar tana da Ahmadu Musa Kida a matsayin mataimakin shugaban kamfanin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Bukaci Hukumar IAEA Ta Bayyana Matsayinta A Shirin Makamashin Nukliya Na Kasar
  • Shugaban Tinubu Ya Tube Kyara A Matsayin Shugaban Kamfanin NNPC Ya Kuma Sannan Ya Maye Gurbinsa
  • DAGA LARABA: Dalilan Da ’Yan Arewa Ke Tafiya Kudu Farauta
  • Duk Da Hanin Gwamna Da ‘Yansanda, Natasha Ta Isa Gida Kuma Ta Yi Taro
  • Ana Zaman Dar-dar A Kasar Zimbabwe Saboda Shirin Zanga-zangar Tsofaffin Sojaji
  • DG VON Yayi Kira Ga Zaman Lafiya Da Hadin Kai Don Fadada Ci gaban Tattalin Arziki Da Ci Gaba.
  • Jiragen Yakin Amurka Sun Kai Sabbin Hare-Hare Kan Kasar Yemen A Daren Jiya
  • Iran: Amurka ta hada kai da Isra’ila wajen kawo cikas ga harkar tsaro a gabas ta tsakiya
  • Farashin fetur ya ƙaru sakamakon hana Dangote mai a Naira
  • Girgizar Kasa: Shugaban Kasar Myanmar Ya Mika Godiya Ga Tawagar Likitocin Yunnan Ta Kasar Sin