Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-03-03@09:19:18 GMT

Kasar Sin Za Ta Zuba Jari A Karamar Hukumar Birnin Kudu

Published: 31st, January 2025 GMT

Kasar Sin Za Ta Zuba Jari A Karamar Hukumar Birnin Kudu

Karamar Hukumar Birnin kudu ta jihar Jigawa ta bada tabbacin hada kai da duk wata hukuma ko kamfani dake da muradin cigaban yankin.

Shugaban karamar hukumar, Dr. Muhammad Uba Builder ya bada wannan tabbacin lokacin da wakilan rukunin kamfanonin kasar Sin wato China suka ziyarce shi a ofishinsa.

Yace karamar hukumar Birnin kudu tana sahun gaba wajen zaman lafiya da karbar baki a fadin jihar.

Mista Sheng ya shaidawa shugaban karamar hukumar niyyar sa ta kafa kamfanin sarrafa takin zamani a yankin domin bunkasa aikin gona.

Yana mai cewar zai samar da kamfanin yin kujeru da gado da sauran kayayyaki domin bunkasa al’amuran kasuwanci a yankin.

Yace zai kuma samar da sinadarin da zai taimakawa manoma wajen samun amfanin gona mai yawa a lokutan noman rani har ma da na damina.

Wakilinmu ya bamu rahoton cewar, a fanin lafiya kuwa, a zancen da ake yi yanzu, hukumar kula da lafiya matakin farko ta karamar hukumar Birnin kudu da hukumar kula da lafiya ta majalisar dinkin duniya sun yabawa shugaban karamar hukumar bisa kokarinsa na tallafawa al’amuran rigakafi a yankin.

Manajan hukumar Alhaji Bello Abdulkarim wanda ya jagoranci tawagar hukumomin biyu zuwa ofishin shugaban karamar hukumar, ya danganta nasarorin da ake samu bisa hadin kai da goyon bayan shugaban wajen gudanar da ayyukan rigakafi a yankin.

Da yake mai da jawabi, shugaban karamar hukumar Alhaji Muhammad Uba Builder, ya bada tabbacin ci gaba da tallafawa harkokin kiwon lafiya bisa la’akkari da muhimmacin ta.

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Kasar Sin Zuba Jari shugaban karamar hukumar karamar hukumar Birnin

এছাড়াও পড়ুন:

Lavrov Ya Yi Watsi Da Batun Aike Wa Da Dakarun Zaman Lafiya A Kasar Ukiraniya

Ministan harkokin wajen kasar Rasha Sergey Lavrov ya yi watsi da batun aike wa da dakarun zaman lafiya zuwa kasar Ukiraniya kamar yadda kasashen turai suke tattaunawa akai.

Ministan harkokin wajen kasar ta Rasha ya bayyana cewa, gwamnatin Amurka tana son a kawo karshen yaki, da shimfida zaman lafiya,amma kuma kasashen turai suna son a ci gaba da yaki.

Sergey Lavro ya kuma ce; tunanin aikewa da dakarun zaman lafiya zuwa Ukiraniya wauta ce.

Lavrov ya bayyana shugaban kasar Ukiraniya Zelenskiy

 da cewa dan Nazi ne, wanda ya ha’inci al’ummarsa.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Lavrov Ya Yi Watsi Da Batun Aike Wa Da Dakarun Zaman Lafiya A Kasar Ukiraniya
  • Yan Ta’adda Sun kashe Sojojin Sa Kai Na Basij Biyu A Yankin Kudu Maso Gabacin Kasar Iran
  • Kasashen Afirka ta Kudu da Malaysia da Colombiya za su hana jiragen ruwa da ke dauke da makamai zuwa Isra’ila
  • Tsohon shugaban hukumar NYSC ya kuɓuta daga hannun ’yan bindiga
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Masallacin Juma’a A Garin Samamiya Da Ke Birnin Kudu
  • Hukuma ta kama ciyaman kan zargin badaƙalar filin N100m a Kano
  • Kasashen Afrika Ta Kudu, Malasiya Da Colombia Zasu Hana Jiragen Ruwa Dauke Da Makamai Tsayawa A Tashoshin Jiragen Ruwansu
  • Kwastam Da Hukumar NPA Sun Kulla Hadakar Bunkasa Ingancin Aiki A Tashoshin Jiragen Ruwa
  • Wata Mujalla Ta Zabi Shugaban NPA A Matsayin Gwarzonta Na Shekarar 2025
  • NAHCON Ta Naɗa Sabon Sakatare