Kotun Kasa Da Kasa Zata Fitar Da Sammacin kama Masu Hannu A Aikata Muggan Laifuka A Darfur Na Sudan
Published: 31st, January 2025 GMT
Kotun da ke shari’ar manyan laifuka a duniya tana gab da fitar da sammacin neman kama wadanda suka aikata muggan laifukan Darfur na kasar Sudan
Mai gabatar da kara na kotun hukunta manyan laifuka ta duniya, Karim Khan, ya sanar da cewa ofishinsa zai bukaci fitar da sammacin kama wadanda ake zargi da aikata ta’asa a yankin yammacin Darfur na kasar Sudan nan kusa kadan.
Karim Khan ya bayyana wa Kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya cewa: Ana aikata muggan laifuka a yankin Darfur da ke yammacin kasar Sudan a lokacin da muke magana kan halin yankin da kuma kullum rana a matsayin makamin yaki a kasar.
Khan ya kara da cewa hakan ya samo asali ne sakamakon bincike da aka gudanar a tsanake bisa hujjoji da bayanan da ofishinsa ya tattara.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji sun kama shugaban ’yan bindiga, Kachallah Hassan Nabamamu a Zamfara
Dakarun Sojin ‘Operation FANSAN YANMA’, sun kama Ƙasurgumin Shugaban ’Yan Bindiga, Kachallah Hassan Nabamamu, wanda ya addabi al’ummar Mada, Tsafe, da wasu yankunan Jihar Zamfara.
Dakarun sun kai farmaki Hegin Mahe, Ruwan Bore, garin Mada, a Ƙaramar Hukumar Gusau a ranar 27 ga watan Fabrairu.
Cibiyar bincike ta nemi a tabbatar da dokar kare haƙƙin mata a Arewa Rage Albashi: Abba ya dakatar da muƙaddashin shugaban ma’aikatan KanoBayan musayar wuta, sojoji sun kashe wasu ’yan bindiga, yayin da Nabamamu ya tsere zuwa cikin wani gida, amma daga ƙarshe dakarun suka cafke shi.
Bayan kama shi, ɗaya daga cikin yaransa, Bakin Malam, ya jagoranci kai harin ramuwar gayya wasu ƙauyuka, wanda ya tilasta wa mazauna ƙauyukan tserewa.
Sai dai dakarun sun mayar da martani, inda suka fatattaki ’yan bindigar, tare da ƙara jibge sojoji don tabbatar da tsaro a yankin.
Nabamamu, ya kasance almajiri ne, daga baya ya zama hatsabibin ɗan bindiga wanda ya yi sanadin ajalin mutane masu yawan gaske.
Ya jagoranci sama da mayaƙa 100, inda yake karɓar haraji daga hannun mazauna wasu ƙauyuka, kuma yana da alaƙa da masu yi wa wasu mahara safarar makamai a yankin.
Kama shi na iya rage ƙarfin ’yan bindiga a Zamfara, yayin da sojoji ke ƙara ƙaimi domin kawar da barazanar tsaro da tabbatar da zaman lafiya a yankin.