Kungiyar Hamas Ta Lashi Takwabin ‘Yantar Da Fursunonin Falasdinawa
Published: 31st, January 2025 GMT
Kungiyar Hamas ta jaddada cewa: Za ta yi aiki da dukkan karfi da azamarta har sai ta raba fursunonin Falasdinawa da gidajen yarin ‘yan mamayar Isra’ila
Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ta jaddada cewa: Za ta yi aiki da dukkan karfi da azamarta har sai ta raba fursunonin Falasdinawa da gidajen yarin ‘yan sahayoniyya, tare da yin nuni da cewa, za ta ci gaba da kokarinta ba tare da wata matsala ba, domin kubutar da su ta kowace hanya.
Kungiyar Hamas ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ta fitar a a yayin bikin sakin wani sabon rukunin fursunonin Falasdinu, tana jaddada cewa: Hamas ta sake sanar da babban alfahari da girmamawa ga al’ummar Falastinu masu tsayin daka, a daidai lokacin da aka sako wani sabon rukunin fursunonin Falasdinawa wadanda suke jarumai daga gidajen yarin yahudawan sahayoniyya, bayan gwagwarmaya ta tilasta musu bude kofofin gidajen yarinsu domin sake Falasdinawa, kuma karkashin yarjejeniyar dakatar da wuce gona da iri da musayar fursunoni.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: fursunonin Falasdinawa
এছাড়াও পড়ুন:
Masar ta miƙa wa Hamas da Isra’ila tayin tsagaita wuta
Ƙungiyar Hamas ta ce tana goyon bayan komawa yarjejeniyar tsagaita wuta a Zirin Gaza, tana mai cewa za ta yi amfani da shawarar da masu shiga tsakanin suka bayar wadda za ta kai ga sakin ƙarin fursunonin Isra’ila biyar da kuma tsagaita wuta a Gaza tsawon kwana 50.
Babban jami’in Hamas da baya zaune a Gaza, Khalil al-Hayyam, ya ce ƙungiyar ta amince da ƙudirin da masu shiga tsakani daga Masar da kuma Qatar suka gabatar.
Miji ya kama matarsa da kwarto ta na’urar drone Ladubban Ranar Idin Karamar SallahOfishin firaiministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu ma ya ce ya karɓi tayin, amma ya gabatar da nasa tayin ”wanda ya ci karo da wanda masu shiga tsakanin suka gabatar masa, a ƙarƙashin jagorancin Amurka.”
BBC ya ruwaito cewa idan har ya tabbata, sabon shirin tsagaita wutar ya zo daidai da bakin ƙaramar Sallah da musulmai suka fara a ranar Lahadi.
A ranar Asabar, ofishin Nethanyahu ya ce ya yi zaman tuntuɓa game da sabon tayin da masu shiga tsakani suka gabatar masa.
Ya kuma ce ya gabatar da nasa sharaɗin, wanda Amurka ta yi amanna da shi, duk da cewa ofishin bai yi ƙarin bayani a kai ba. Itama Amurka ba ta kai ga cewa komai ba a kai kawo yanzu.
Wannan na zuwa ne yayin da dakarun Isra’ila suka ƙaddamar da sabbin hare-hare a Rafah da sassan Gaza bayan ƙarewar wa’adin tsagaita wutar da aka ƙulla a ranar 19 ga watan Janairu tsakanin ɓangarorin.
Tun bayan ƙarewar wa’adin har yanzu ɓangarorin sun gaza amincewa da fara aiwatar da zango na biyu na yarjejeniyar tsagaita wutar.
A zangon farko na yarjejeniyar tsagaita wutar dai Hamas ta saki ƴan Isra’ila 33, kuma har yanzu tana ci gaba da riƙon wasu 59, duk da dai ana zaton wasu daga cikin su sun mutu.
A baya dai Hamas ta haƙiƙance kan aiwatar da yarjejeniyar a yadda take tun farko, da kuma tattauna zango na biyu wanda zai kai ta ga sakin sauran mutanen da ta yi garkuwa da su, da kuma kawo ƙarshen yaƙin baki ɗaya ta hanyar janyewar dakarun Isra’ila daga Gaza.
Sai dai Isra’ila da Amurka sun nemi a tsawaita wa’adin zangon farko na yarjejeniyar wanda ya ƙare a watan da ya gabata, ba tare da fayyace yadda za a kawo ƙarshen yaƙin ba.