HausaTv:
2025-02-27@01:25:40 GMT

Kungiyar Hamas Ta Lashi Takwabin ‘Yantar Da Fursunonin Falasdinawa

Published: 31st, January 2025 GMT

Kungiyar Hamas ta jaddada cewa: Za ta yi aiki da dukkan karfi da azamarta har sai ta raba fursunonin Falasdinawa da gidajen yarin ‘yan mamayar Isra’ila

Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ta jaddada cewa: Za ta yi aiki da dukkan karfi da azamarta har sai ta raba fursunonin Falasdinawa da gidajen yarin ‘yan sahayoniyya, tare da yin nuni da cewa, za ta ci gaba da kokarinta ba tare da wata matsala ba, domin kubutar da su ta kowace hanya.

Kungiyar Hamas ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ta fitar a a yayin bikin sakin wani sabon rukunin fursunonin Falasdinu, tana jaddada cewa: Hamas ta sake sanar da babban alfahari da girmamawa ga al’ummar Falastinu masu tsayin daka, a daidai lokacin da aka sako wani sabon rukunin fursunonin Falasdinawa wadanda suke jarumai daga gidajen yarin yahudawan sahayoniyya, bayan gwagwarmaya ta tilasta musu bude kofofin gidajen yarinsu domin sake Falasdinawa, kuma karkashin yarjejeniyar dakatar da wuce gona da iri da musayar fursunoni.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: fursunonin Falasdinawa

এছাড়াও পড়ুন:

Kasashen Kawancen Sahel Sun Kadaddamar Da Tutar Kungiyar

Kasashen nan guda uku mambobin kungiyar kawancen Sahel (AES) da suka balle daga kungiyar ECOWAS, sun kaddamar da tutarsu ta bai daya.

An kadaddamar da tutar ne a yayin haduwar ministocin harkokin wajen kasashen jiya Asabar a Bamako babban birnin kasar Mali mai rike da shugabancin kungiyar na farko.

Firaministan Mali, Janar Abdoulaye Maïga ya bayyana a yayin bikin, cewa “Tutar kungiyar AES, launin kore, tana dauke da tambarin kungiyar a tsakiyarta.”

 Ya jaddada cewa launin kore yana nuna alamar bege da wadata, wanda ke wakiltar dukiya da karfin tattalin arziki.

Wannan sabuwar alamar ta kunshi hadin kai da muradin bai daya na kasashen uku, inda suka kuduri aniyar yin aiki tare domin bunkasa tattalin arziki da zamantakewar yankin inji shi.

Kaddamar da wannan tuta na zuwa ne kasa da wata guda bayan da aka kaddamar da fasfo din kungiyar a ranar 29 ga watan Janairun 2025, Da nufin karfafa hadin gwiwarsu da saukaka zirga-zirgar jama’a da kayayyaki cikin ‘yanci a cikin yankin.

Wannan taron, wanda wani bangare ne na taron ministocin da ke ci gaba da gudana har zuwa ranar 23 ga watan Fabrairu, ya tabbatar da aniyar Mali, Burkina Faso da Nijar na kulla kawance mai karfi da ‘yanci, bayan ficewarsu daga ECOWAS da suak zarga da zama ‘yar amshin shatan kaashen yamma musamman faransa wacce ta yi musu mulin mallaka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamas Tace An Cimma Matsaya Da HKI Bayan Tsekon Da Aka Samu Na Sakin Fursinoni Falasdinawa 620
  • Xi Ya Jaddada Cewa Dole Ne A Dauki Sabbin Nauyi Da Sabbin Ayyuka A Sabuwar Tafiya Ta Inganta Zamanintarwa Irin Ta Kasar Sin
  • An Cimma Matsaya Kan Sakin Fursunonin Falasdinawa 206 Da Isra’ila Ta Jinkirta
  • Hamas ta yi tir da matakin Isra’ila na shirin takura masu ibada a masallacin Quds
  • Sin Ta Jaddada Kudurin Hadin Gwiwa Da Kasa Da Kasa Kan Hakkin Dan Adam
  • Rasha : Putin Ya Ce Turawa ‘Na Iya Shiga’ A Sasanta Rikicin Ukraine
  • Kasashen Kawancen Sahel Sun Kadaddamar Da Tutar Kungiyar
  • Kungiyar Hamas Ta Dakatar Da Tattaunawa Da HKI Har Zuwa Sakin Fursinoni Falasdinawa
  • Hamas ta yaba da irin goyon bayan da Sayyed Nasrallah ya baiwa Falasdinu
  • Kungiyar RSF da kawayenta na shirin kafa gwamnatin ‘yan tawaye a Sudan