HausaTv:
2025-03-03@16:52:07 GMT

Kungiyar Hams Ta Jinjinawa Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Kan Goyon Bayan Gwagwarmaya

Published: 31st, January 2025 GMT

Kungiyar Hamas ta yaba da rawar da Iran ke takawa wajen tallafawa al’ummar Falasdinu masu neman ‘yanci kai

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya gana da wata tawaga daga jagororin kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas, karkashin jagorancin shugaban majalisar gudanarwa (wanda aka kafa bayan kisan jagoran kungiyar Yahya Sinwar) Mohammed Darwish, a babban birnin Qatar, Doha a jiya Alhamis.

Sanarwar da kungiyar Hamas ta fitar ta bayyana cewa, tawagar kungiyar ta hada da shugabannin Khalil Al-Hayya, Hussam Badran, Izzat Al-Rishq da Basem Na’im.

Darwish ya yaba da rawar da Iran ta taka wajen tallafa wa al’ummar Falasdinu masu neman ‘yancin kai, yana mai jaddada cewa: “Harin Daukan Fansa naAmbaliysar Al-Aqsa Mai Albarka” wani ci gaba ne a yunkurin al’ummar Falasdinu na fatattakar ‘yantar da kai daga ‘yan mamayar Isra’ila.”

Ya kuma jaddada cewa: “Shirye-shiryen da mafarkin da gwamnatin mamayar Isra’ila suke yi na kawar da al’ummar Falasdinu daga kasarsu ta gado ta hanyar kaddamar da yaki da kashe-kashe ta kowane irin nau’in ta’addanci, ba zasu taba amfani ba, kuma al’ummar Falasdinu sun kafu ne a cikin kasarsu, suna sadaukar da kai ne domin hakkinsu da Qudus da kuma Masallacin Al-Aqsa”.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: al ummar Falasdinu

এছাড়াও পড়ুন:

An Yi Jana’izar Shahidan kungiyar Hizbullah Fiye Da 120 Kudancin Kasar Lebanon A Yau Jumma’a

Shadidan Hizbullah kimabi 130 ne aka yi jana’izarsu a yau jumma’a a kudancin kasar Lebanon. Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran tanakalto kungiyar Hizbullah na fadar haka, ya kuma kara da cewa kungiyar ta gabatar da shihidar da dama saboda kare kasarsu, saboda kare kasar Lebanon daga mamayar HKI.

Labarin ya kara da cewa an gudanar da jana’izar ne a garuruwan Aitarun da kuma Aita shaab. Inda mutanen da dam dagayankin zuka halarta . Labarin ya kara da cewa Shahidan sun kai ga shahada ne a hare-haren da sojojin HKI suka kai kan kudancin kasar ta Lebanon a cikin watannin Octoba da kuma Nuwamba na shekara ta 2024.

Labarin ya kara da cewa a yakin dai mutanen leabin kimani 4000 ne suka rasa rayukansu mafi yawansu fararen hula ne wadanda basu san hawa ko sauka ba.

Kafin jana’izar yau ma, sojojin HKI da suke mamaye da wasu wurare a kudancin kasar Lebanon sun yi harbi da bindiga don tsoratar da mutane masu Jana’izar, wanda hakan ya kasance keta yarjeniyar da aka kulla da Ita

A dai dai lokacin ne sojojin HKI ta kashe manya-manyan shuwagabanni da kwamandojojin sojojin Hizbullah na kasar wanda ya hada har da shugaban kungiyar Sayyid Hassan Nasarallah, da magajinsa Sayyid Hashin Safiyyuddiin, wadanda aka yi masu jana’iza a ranakin 23-24 na watan fabarairu da muke ciki a birnin Neirut babban birnin kasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamas: Babu Wani Karin Tattaunawa Da HKI, A Aiwatar Da Yarjeniyar Kamar Yadda Take
  • Nijar: An Kashe Sojoji 11 A Wani Hari Na Kungiyar al-Ka’ida
  •  Hamas: Matakin Netenyahu Na Dakatar Da Shigar Kayan Agaji Cikin Gaza Keta Yarjejeniya Ne
  • Ta ina Kungiyar Hizbullah ke samun kuɗaɗenta?
  • Shin Liverpool Za Ta Kai Labari Ba Tare Da Muhammad Salah Ba?
  • Al-Houthi : Isra’ila Na fakewa Da Goyan Bayan Amurka Tana Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza
  • Yemen Ta Ce A Shirye Take Ta Koma Yaki Idan Yaki Ya Sake Barkewa A Gaza
  • Hukumar Lamuni Ta Duniya IMF Da Bankin Duniya Sun Ce Bazasu Taimakawa Lebanon Ba Sai Da Sharudda
  • Kungiyar Kare Hakkin Bil’adama ta ‘Euro-Med Monitor’ Ta Ce Ta Sami Shaidu Wadanda Suka Tabbatar Da Cewa HKI Tana Azabtar Da Fulasdinwa
  • An Yi Jana’izar Shahidan kungiyar Hizbullah Fiye Da 120 Kudancin Kasar Lebanon A Yau Jumma’a