Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta Sanar da cewa: Ma’aikatar tsaron kasar ta kebe jirgin saman maras matuki ciki kirar “Arash-2” da ta kera ne don kai hari kan haramtacciyar kasar Isra’ila

A ci gaba da gudanar ranakun atisayen soji domin ayyukan tsaron kasa, da sojojin Iran suke gwajin kai hare-hare da kuma sarrafa manyan na’urorin makaman tsaro a yankin da ke yammacin kasar, a karon farko sun nuna wasu jiragen saman yaki maras matuki ciki da aka kera a cikin gida masu tsnanin karfin munanan hare-hare irin na kunan bakin wake kirar “Ababil” da “Arash-2” da dakarun sojin kasar Iran zasu yi amfani da su wajen kare tsaron kasa duk lokacin da ya dace.

Jiragen saman “Ababil” ne suka jagoranci tawagar sabbin makaman, sannan wasu jiragen saman kunar bakin wake guda uku na “Arash” suka biyo bayansu, wadanda idan aka kai hari da su zasu tarwatsa wuraren da aka tura su.

Abin lura shi ne cewa: “jirgin Arash-2 yana ci nisan kilomita 2,000, wanda ya sa ya zama jagora a tsakanin takwarorinsa na jiragen saman yakin Iran da ma duniya baki daya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Yemen Ta Ce A Shirye Take Ta Koma Yaki Idan Yaki Ya Sake Barkewa A Gaza

Shugaban kungiyar Ansarullah Sayyid Abdulmalik Badruddeen Huthi ya bayyana cewa kasar Yemen a shirye take ta sake shiga yaki idan yarjeniyar tsagaita wuta tsakanin bangarorin biyu ta wargaje.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Sayyid Huthi yana fadar haka a wani jawabin da ya gabatar ta hotunan bidiyo a jiya 28 ga watan Fabrairun shekara ta 2025.

Shugaban kungiyar ta Ansarullah ya bayyana cewa birnin Tel’aviv wato Yafa, zai zama babban wurin da makaman kungiyar zasu nufi idan hakan ya faru.

Huthi ya ce “Idan yaki ya sake barkewa za mu kai hare-hare a ko ina a HKI sannan birnin Tel’aviv zai za ma babbar manufar makamammu.

Yace: Kasar Yemen ta na kallom yadda al-amura suke tafiya a ayyukan tsagaita wutar, kuma ta na kallon yadda HKI take sabawa wasu abubuwan da ke cikin yarjeniyar. Ya kuma ambaci yadda HKI ta ki janyewa daga rafah da kuma yankin philidelfiya na kan iyaka da kasar Masar. Wanda kuma ya sabawa yarjeniyar. Sannan ya kammala da cewa gwamnatin kasar Amurka ta na kodaitar da HKI da yin hakan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwance Damarar Dakarun Hashdu Zai Ragewa Harkokin Tsaron Kasar Iraki Aminci
  • Masana Fasahar Gina Jiragen Sama A Iran Sun Samar Da Wata Fasahar Nano Mai Rage Nauyin Jiragen Sama
  • Lavrov Ya Yi Watsi Da Batun Aike Wa Da Dakarun Zaman Lafiya A Kasar Ukiraniya
  • Nijar: An Kashe Sojoji 11 A Wani Hari Na Kungiyar al-Ka’ida
  • Kasashen Afirka ta Kudu da Malaysia da Colombiya za su hana jiragen ruwa da ke dauke da makamai zuwa Isra’ila
  • Ma’aikatar Tsaron Jama’ar Sin Na Matukar Adawa Da Barazanar Da Amurka Ta Yi Na Karin Haraji
  • Yemen Ta Ce A Shirye Take Ta Koma Yaki Idan Yaki Ya Sake Barkewa A Gaza
  • Kasashen Afrika Ta Kudu, Malasiya Da Colombia Zasu Hana Jiragen Ruwa Dauke Da Makamai Tsayawa A Tashoshin Jiragen Ruwansu
  • Kwastam Da Hukumar NPA Sun Kulla Hadakar Bunkasa Ingancin Aiki A Tashoshin Jiragen Ruwa
  • Wata Mujalla Ta Zabi Shugaban NPA A Matsayin Gwarzonta Na Shekarar 2025