Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Kebance Jiragen Saman Yaki Na Kai Hari Kan ‘Yan Sahayoniyya
Published: 31st, January 2025 GMT
Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta Sanar da cewa: Ma’aikatar tsaron kasar ta kebe jirgin saman maras matuki ciki kirar “Arash-2” da ta kera ne don kai hari kan haramtacciyar kasar Isra’ila
A ci gaba da gudanar ranakun atisayen soji domin ayyukan tsaron kasa, da sojojin Iran suke gwajin kai hare-hare da kuma sarrafa manyan na’urorin makaman tsaro a yankin da ke yammacin kasar, a karon farko sun nuna wasu jiragen saman yaki maras matuki ciki da aka kera a cikin gida masu tsnanin karfin munanan hare-hare irin na kunan bakin wake kirar “Ababil” da “Arash-2” da dakarun sojin kasar Iran zasu yi amfani da su wajen kare tsaron kasa duk lokacin da ya dace.
Jiragen saman “Ababil” ne suka jagoranci tawagar sabbin makaman, sannan wasu jiragen saman kunar bakin wake guda uku na “Arash” suka biyo bayansu, wadanda idan aka kai hari da su zasu tarwatsa wuraren da aka tura su.
Abin lura shi ne cewa: “jirgin Arash-2 yana ci nisan kilomita 2,000, wanda ya sa ya zama jagora a tsakanin takwarorinsa na jiragen saman yakin Iran da ma duniya baki daya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran ta mayar wa Amurka martani kan barazanar kai mata hari
Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya yi kakkausan gargaɗi kan barazanar Amurka da ƙawayenta na kai wa ƙasarsa hari.
Khamenei ya sha alwashin maida mummunar martani idan har Amurka da ƙaddamar da hare-hare a ƙasar ta Iran.
Gargaɗin nasa martani ne kan barazanar da Shugaban Amurka Donald Trump ya yi wa ƙasar cewa za su kai mata hari.
Muna jiran ganin hukuncin da za a ɗauka kan kashe ’yan Arewa a Edo — Sarkin Musulmi Kisan Mafarauta: Matakan da gwamnatin Edo da ta Kano suke ɗauka“Suna yi min barazana, kuma idan suka sake suka kawo min hari tabbas zan rama,” in ji shi.
Yayin wata tattaunawa a ranar Asabar ne Trump ya yi alƙawarin kai wa Iran ɗin hari matuƙar ba ta amince da yarjejeniyar makamin ƙare dangin ba.
“Idan ba su amince da sabuwar yarjejeniyar makaman ƙare dangin ba, za mu tada bama-bamai,” in ji Trump.
Sai dai bai bayyana ko Amurkan ce za ta kai harin ba ko kuma ƙawarta Isra’ila.
To sai dai cikin wani saƙo da ya wallafa a shafin X, kakakin ma’aikatar wajen Iran Esmaeil Baqaei ya ce barazanar ta Trump a bainar duniya yana matsayin shugaban kasa abin mamaki ne, kuma babbar barazana ce ga zaman lafiya da tsaron ƙasa da ƙasa.