HausaTv:
2025-04-02@14:49:29 GMT

Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Jaddada Bukatar Bunkasa Alakarta Da Kasar Qatar

Published: 31st, January 2025 GMT

Ministan harkokin wajen Iran ya jaddada aniyar Iran na bunkasa alaka da kasar Qatar a dukkan fannoni

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya yi nuni da kyakkyawar alakar da ke tsakanin Iran da Qatar, yana mai jaddada aniyar gwamnatin Jamhuriyar Musulunci ta Iran na bunkasa alaka da kasar Qatar a fannoni daban daban.

Wannan ya zo ne a yayin ganawar da ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya yi a birnin Doha a jiya Alhamis, tare da fira ministan Qatar kuma ministan harkokin wajen kasar Sheikh Mohammed bin Abdulrahman Al- Thani.

Taron ya tattauna batutuwa da dama da suka shafi bangarorin biyu, da suka hada da ci gaban huldar dake tsakanin kasashen biyu, da kuma ci gaban yankin, musamman a fagen Falasdinawa bayan yarjejeniyar tsagaita bude wuta, da kuma yanayin siyasar kasar Lebanon bayan zaben shugaban kasa da fira minista.

Tattaunawar ta ta’allaka ne kan keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta da yahudawan sahayoniyya suka yi, da kuma abubuwan da suke faruwa a kasar Siriya, sun kuma tattauna tare da yin musayar ra’ayi kan yadda kasashen biyu ke ba da goyon baya ga ‘yancin kai, kwanciyar hankali da kuma ‘yancin yankin kasar Siriya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: harkokin wajen

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Gano Babban Yankin Hakar Danyen Mai A Tekun Kudancin Kasar

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Basakkwacen da ya yi ridda ya sake karɓar addinin Musulunci
  • Kasar Sin Za Ta Yi Ramuwar Gayya Kan Takunkumin Biza Da Amurka Ta Kakaba Wa Jami’anta
  • Wang Yi Ya Jinjina Wa Gudummawar Da Sinawa Da ’Yan Rasha Suka Bayar A Yakin Duniya Na Biyu
  •  Larijani:  Dole Iran Ta Kera Makaman Nukiliya Idan Amurka Da Isra’ila Su Ka Kawo Ma Ta Hari
  • Sin Ta Gano Babban Yankin Hakar Danyen Mai A Tekun Kudancin Kasar
  • Jagora : A yau, duniyar musulmi tana bukatar hadin kai
  • Iran ta gargadi Amurka kan barazanar harin bam da Trump ya yi
  • Kasar Sin Ta Jaddada Bukatar Karfafa Cinikayya Da Ketare Tare Da Fadada Bude Kofa
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci: Kasashen Yamma Sune Yan Ta’adda Na Gasliya A Yankin
  • Iran: Amurka ta hada kai da Isra’ila wajen kawo cikas ga harkar tsaro a gabas ta tsakiya