HausaTv:
2025-03-03@09:45:38 GMT

Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Jaddada Bukatar Bunkasa Alakarta Da Kasar Qatar

Published: 31st, January 2025 GMT

Ministan harkokin wajen Iran ya jaddada aniyar Iran na bunkasa alaka da kasar Qatar a dukkan fannoni

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya yi nuni da kyakkyawar alakar da ke tsakanin Iran da Qatar, yana mai jaddada aniyar gwamnatin Jamhuriyar Musulunci ta Iran na bunkasa alaka da kasar Qatar a fannoni daban daban.

Wannan ya zo ne a yayin ganawar da ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya yi a birnin Doha a jiya Alhamis, tare da fira ministan Qatar kuma ministan harkokin wajen kasar Sheikh Mohammed bin Abdulrahman Al- Thani.

Taron ya tattauna batutuwa da dama da suka shafi bangarorin biyu, da suka hada da ci gaban huldar dake tsakanin kasashen biyu, da kuma ci gaban yankin, musamman a fagen Falasdinawa bayan yarjejeniyar tsagaita bude wuta, da kuma yanayin siyasar kasar Lebanon bayan zaben shugaban kasa da fira minista.

Tattaunawar ta ta’allaka ne kan keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta da yahudawan sahayoniyya suka yi, da kuma abubuwan da suke faruwa a kasar Siriya, sun kuma tattauna tare da yin musayar ra’ayi kan yadda kasashen biyu ke ba da goyon baya ga ‘yancin kai, kwanciyar hankali da kuma ‘yancin yankin kasar Siriya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: harkokin wajen

এছাড়াও পড়ুন:

Masar ta ki amincewa da duk wani yunkuri na kafa gwamnatin ‘yan adawa a Sudan

Masar ta jaddada matsayinta kan duk wani yunkuri na kawo barazana ga hadin kan Sudan da ‘yancin kanta da kuma yankinta, tare da yin gargadin cewa kafa gwamnatin rikon kwarya na iya kawo rudani a kasar.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a jiya Lahadi, Ma’aikatar harkokin wajen Masar ta sanar da cewa “Jamhuriyar Larabawa ta Masar ta yi watsi da duk wani mataki da ke kawo barazana ga hadin kan Sudan, ciki har da yunkurin kafa gwamnatin ‘yan adawa, saboda hakan zai kara dagula al’amuran siyasa da kuma kawo cikas ga kokarin hada kan kasar.

Alkahira ta bukaci dukkan bangarorin da su yi aiki mai inganci tare da cikakken tsari na siyasa, da nufin cimma daidaito da kuma maido da tsaro a fadin kasar.

Ta kara da cewa, “Masar ta bukaci dukkan sojojin Sudan da su ba da fifiko ga cin moriyar kasa mafi girma da kuma taka rawar gani wajen bullo da wani cikakken tsari da zai kawo hadin da daidaito ba tare da nuna banbanci ko tsoma bakin kasashen waje ba.”

Ministan harkokin wajen Sudan Ali Youssef al-Sharif ya tabbatar a karshen watan da ya gabata cewa “babu wanda zai amince da abin da ake kira gwamnatin hadaka a Sudan, kuma babu wata kasa da za ta amince da ita.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran: Majalisar dokoki ta tsige ministan tattalin arziki saboda hauhawar farashi
  • Masar ta ki amincewa da duk wani yunkuri na kafa gwamnatin ‘yan adawa a Sudan
  • Kasashen Somaliya Da Habasha Suna Gab Da Rattaba Hannu Akan Amfani Da Tashar Jirgin Ruwa
  • Yan Ta’adda Sun kashe Sojojin Sa Kai Na Basij Biyu A Yankin Kudu Maso Gabacin Kasar Iran
  • Xi Ya Jaddada Ciyar Da Shirin Kasar Sin Mai Kwanciyar Hankali Zuwa Babban Mataki
  • Iran Ta Zama Zakara A Damben Gargajiya Ta 2025 UWW Wanda Aka Gudanar A Kasar Albaniya
  • Iran Da Haddiyar Daular Larabawa Sun Gudanar Da Taron Kwamitin Siyasa Da Al-adu Na Kasashen Biyu
  • Habasha Da Somaliya Sun Tattaunawa Hanyoyin Sake Mayar Da Alaka
  • Yawan ’Yan Kasashen Waje Da Suka Shigo Kasar Sin Ba Tare Da Biza Ba A Bara Ya Ninku
  • Kasashen Habasha da Nijar sun tattauna kan inganta hadin gwiwar soji da tsaro