Leadership News Hausa:
2025-03-03@16:39:08 GMT

Ana ɗar ɗar Kan Mutuwar Sojoji Bayan Da Tirela Ta Kwace A Legas

Published: 31st, January 2025 GMT

Ana ɗar ɗar Kan Mutuwar Sojoji Bayan Da Tirela Ta Kwace A Legas

Wani direba da ake zargin yana cikin maye ya kutsa da motarsa cikin wani gungu na sojoji daga barikin Myoung da ke Yaba dake jihar Legas, yayin da suke atisayen motsa jiki da safiyar yau Juma’a, lamarin da ake jin tsoron cewa ya yi sanadiyyar mutuwar Sojojin da dama.

Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya haifar da tashin hankali a cikin sansanin Sojojin.

Wani Soja da ya tsira daga harin ya bayyana cewa, “Jini ne ko’ina. Na tsira ne kawai saboda ina baya.”

Mun Kashe Ƴan Ta’adda Sama Da 70, Kafin Mu Yi Rashin 22 – Sojoji Sojoji Sun Ƙwato Makamai, Sun Ci Gaba Da Neman Bello Turji A Zamfara

Sojan (wanda ba a bayyana sunansa ba) ya ce a cikin motar akwai matasa uku da ake zargin ‘yan damfara ne, masu amfani da intanet (Yahoo Boys). Bayan hatsarin, ɗaya daga cikinsu ya tsere, yayin da sauran biyun aka kama su, aka yi musu dukan tsiya, tare da lalata motarsu.

Zamu kawo cikakken labarin nan gaba…

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Al-Houthi : Isra’ila Na fakewa Da Goyan Bayan Amurka Tana Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza

Shugaban kungiyar Ansarallah ta kasar Yemen Sayyed Abdul-Malik Al-Houthi, ya bayyana cewa Isra’ila na fakewa da goyan bayan Amurka tana keta yarjeejniyar tsagaita wuta a Gaza.

Al-Houthi ya bayyana cewar: Kin janyewar makiya daga yankin Rafah, ya zamanto karara karya yarjejeniyar da aka kulla tsakanin Masar da makiya yahudawan sahyoniya. »

Ya kara da cewa: gazawar ‘yan mamaya na janyewa daga yankin Rafah na nuni da wata barazana mai hatsari ga al’ummar Falastinu da gwamnati da sojojin Masar. »

Jagoran kungiyar ta Ansarullah ya jaddada cewa: Makiya ba su cika bangare mai yawa na alkawurran da suka dauka ba, musamman a fagen ayyukan jin kai, sannan kuma suna yin watsi da sauran alkawurran da suka dauka, musamman na ficewa daga yankin Rafah. »

Al-Houthi ya kara da cewa: Haka nan makiya yahudawan sahyoniya ba su janye gaba daya daga kudancin kasar Labanon ba, wanda ya zama mamaya da kuma barazana ga al’ummar kasar Lebanon da kuma keta  hurimin kasar. »

Zamu zura ido mu gani, kuma dole ne mu kasance cikin shiri,” in ji jagoran kungiyar Ansarallah ta kasar Yemen.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ya rasu a yayin buɗa-baki a Abuja
  • Zargin Neman Yin Lalata: Ina Da Kwararan Hujjoji Akan Akpabio – Natasha 
  • Nijar: An Kashe Sojoji 11 A Wani Hari Na Kungiyar al-Ka’ida
  • Kare ya ta da gobara a gida
  • An kama ɓarayin waya a Kano
  • Al-Houthi : Isra’ila Na fakewa Da Goyan Bayan Amurka Tana Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza
  • Gobara ta ƙone sashen wani asibiti a Legas
  • Tsohon shugaban hukumar NYSC ya kuɓuta daga hannun ’yan bindiga
  • Falalar Ramadan: Wata na rahama, gafara, da tsira daga wuta
  • Sojoji sun kama shugaban ’yan bindiga, Kachallah Nabamamu a Zamfara