Aminiya:
2025-04-02@21:42:48 GMT

An ɗaure zawarawa a gidan yari kan aikata zina

Published: 31st, January 2025 GMT

Kotu ta daure wata matar aure da wani magidanci a gidan yari kan aikata lalata da juna.

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a Abuja ta yanke wa zawararwan hukuncin ɗaurin wata uku kowannensu ne bayan samun su laifin aikata zina da junansu.

Matar mai shekaru 25 da bazawarin mai shekara 30 sun amsa laifin a lokacin da aka karanta musu takardar tuhumar a gaban kotun.

Zawarawan sun kuma buƙaci kotun ta yi musu sassauci.

Da farko alƙalin ya ba da umarnin tsare su har sai sun kawo shaida da za su yi rantsuwa cewa su mutanen kirki ne, amma suka kasa.

Daga bisani Alƙali Olatunji Oladunmoye, ya yanke wa kowannensu hukuncin ɗaurin wata uku ko biyan tarar Naira 25,000.

Tun da farko, ɗan mai gabatar da ƙara, Dabo Yakubu, ya shaida wa kotu cewa waɗanda ake zargin sun amsa laifin a jawabin da suka rubuta a caji ofis, bayan an kawo karar su.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: bazawara bazawari matar aure

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

Haka kuma, an Ƙwato bindiga ƙirar gida da Naira miliyan 4.84 da ake zargin kuɗin fansa ne.

An ceto Dokta Yushau ba tare da wata matsala ba.

A wata arangama daban, jami’an ‘yansanda sun kama wani Kafinta Musa a Jihar Taraba bisa zargin fashi da makami, garkuwa da mutane, da mallakar makamai ba bisa ƙa’ida ba.

An ƙwato bindiga ƙirar AK-49 a hannunsa, kuma ana ci gaba da bincike don kama sauran miyagun da ke tare da shi.

Sufeto-Janar na ‘Yan Sanda, Kayode Egbetokun, ya jinjina wa jami’an da suka gudanar da wannan aikin tare da kira ga al’umma da su ci gaba da ba da bayanan sirri da za su taimaka wajen yaƙi da laifuka.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
  • Tsohon Gwamnan Zamfara Ya Bukaci A Ci Gaba Da Tallafawa Mabukata Bayan Ramadan.
  • Sanata Yari Zai Tallafa Wa Marayu 20,000 A Zamfara
  • Ta zuba wa abokan aikinta guba bayan taƙaddama kan ƙarin matsayi
  • Gwamna Abba Ya Nemi A Bayyana Fuskokin Waɗanda Suka Kashe ‘Yan Arewa A Edo
  • Kungiyar “Amnesty” Na Zargi Netanyahu Da Aikata Laifukan Yaki
  • Faransa : An haramta wa Marie Le Pen, takara har tsawon shekaru 5
  • Muna jiran ganin hukuncin da za a ɗauka kan kashe ’yan Arewa a Edo — Sarkin Musulmi
  • Dan shekara 4 ya kira wa mahaifiyarsa ’yan sanda
  • Wani Asbiti A Amurka Ya Kori Wata Likita Daga Aiki Bayan Ta Yi Allawadai Da Yahudawan Sahyoniyya