Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya yi kira da a gaggauta kwashe yara 2,500 da suka jikkata a yakin da Isra’ila ta kwashe watanni 15 tana yi a Gaza domin samun kulawar gaggawa.

Rokon nasa ya biyo bayan ganawar da ya yi da likitocin Amurka ne wadanda suka yi gargadin cewa yaran na fuskantar barazanar mutuwa a makonni masu zuwa.

Likitocin hudu, wadanda suka yi aikin sa kai a Gaza sun bayyana mummunan halin da yanayin  kiwon lafiyar yankin ke ciki, wanda yakin ya yi wa illa.

Guterres ya ce ya ji dadin matuka  bayan tattaunawarsa da likitocin Amurka ranar Alhamis.  Ya kuma”Dole ne a kwashe yara 2,500 ba tare da bata lokaci ba, tare da ba da tabbacin cewa za su iya komawa ga iyalansu bayan sun samu lafiya, kamar yadda ya rubuta a shafukan sada zumunta.

Kwanaki kadan kafin a fara tsagaita wuta a ranar 19 ga watan Janairu, Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta ba da rahoton cewa sama da Falasdinawa 12,000 ne ke jiran kulawar likitoci, kuma ana zaton cewa za a samu karuwar masu bukatar irin kulawa bayan tsagaita bude wuta.

Daga cikin wadanda ke bukatar agajin gaggawa akwai yara 2,500, a cewar Feroze Sidhwa, wani likitan tiyata daga California wanda ya yi aiki a Gaza daga ranar 25 ga Maris zuwa 8 ga Afrilun bara.

Bayanin ya ce daga cikin yaran 2,500 wasu sun fara mutuwa, kuma za su ci gaba da mutuwa matukar ba a gagaguta dake sub a a cewar Guterres.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

HKI Tana Amfani Yunwa A Matsayin Makamin Yaki  A Kan Falasdinawa A Gaza

Wakilin falasdinawa a kutun kasa da kasa ta ICJ da ke birnin Haque na kasar Nerthelands yace HKI tana amfani da hana kayakin agaji daga ciki har da abinci shiga gaza a matsayin makami kan Falasdinawa don kashesu.

Tashar talabijib ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Ammar Hijazi jakadan kasar Faladinu a cibiyoyin MDD a kasashen Turai yana fadar haka a gaban alkalai a kotun ta ICJ a jiya litinin.

Ya ce  HKI tana kisa ta sama da makamai, sannan tana kisa ta kasa da yunwa banda haka tana ci gaba da korar  Falasdinawa daga yankin yamma da kogin Jordan tun fiye da watanni 3 da sua habata.

Kutun ta bude wannan zaman ne bisa bukatar MDD ta shekara ta 2024 na bincike don tabbatar da cewa HKI tana amfani yunwaa a matsayin makami a Gaza. Ammar Hijazi ya kara da cewa banda wannan babban kotun HKI tana goyon bayan amfani da yunwa a matsayin makami a gaza tun fiye da watanni 2 da suka gabata.

Wasu lauyoyi daga kasashe daban–daban wadanda suka hada da Nerthlands da Afirka ta kudu duk sun yi magana sun kuma yi allawadai da HKI kan abinda take aikatawa a Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • HKI Tana Amfani Yunwa A Matsayin Makamin Yaki  A Kan Falasdinawa A Gaza
  • Har Yanzun Ana Zaman Dar-Dar A Burkina Faso Bayan Kokarin Juyin Mulkin Da Bai SamiNasara Ba
  • Sama Da Masu Sayayya Daga Ketare 220,000 Ne Suka Halarci Bikin Baje Kolin Canton Karo Na 137
  • Aikin Hajji: Za A Fara Jigilar Alhazan Jihar Kwara A Ranar 12 Ga Watan Mayu
  • Iran Da Rasha Sun Jaddada Yin Aiki Tare A Fagen Kiwon Lafiya
  • Fira Ministan Indiya Ya Bayyana Cewa: Iran Tana Kokari A Fagen Inganta Zaman Lafiya A Yanki Da Duniya Baki Daya
  • Falasdinawa 39 Sun Yi Shahada A Cikin Sa’o’I 24
  •  Adadin Wadanda Su ka Kwanta Dama A Gobarar Tashar Jirgin Ruwan Shahid Raja’i Sun Kai 21
  • Hukumar Alhazan Jihar Kaduna Ta Wajibta Gudanarda Binciken Lafiya Ga Maniyatan 2025
  • Daga Kaina An Gama Harkar Fim A Zuri’ata – Moda