Aminiya:
2025-03-03@09:45:38 GMT

Isra’ila ta kashe Palasdinawa 10 ta kama 12 bayan musayar fursunoni 110

Published: 31st, January 2025 GMT

Kungiyar Hamas ta sanar da sunayen mutum uku da za ta mika wa kasar Isra’ila a Gaza a ranar Asabar a ci gaba da musayar fursunonin yaki tsakaninsu.

Bayan sako ’yan Isra’ila uku da ’yan kasar Thailand biyar a ranar Alhamis, Rundunar Qassam , sashen sojin Hamas ta sanar ranar Juma’a cewa wadanda kungiyar za ta sako su ne Ofer Kalderon da Keith Siegel da kuma Yarden Bibas.

Hakan na zuwa ne bayan a cikin dare jiragen yakin Isra’ila sun kashe Palasdinawa 10 a sansanin ’yan gudun hijira na Jenin da ke garin Tammun da ke yankin Yammacin Kogin Jordan.

Kazailka ’yan sandan Isra’ila sun kama Palasdinawa 12 a yankin Gabashin Birnin Kudus a yayin da suke murnar sako ’yan uwansu 110 da Isra’ila ta yi daga gidajen yarinta a wani bangare na yarjejeniyar zaman lafiya a Zirin Gazan.

An ɗaure zawarawa a gidan yari kan aikata zina Tubabbun ’yan Boko Haram 5,000 sun koma cikin jama’a

Jami’an tsaro na Isra’ila na ci gaba da kai hare hare da tsare Palasdinawa ne duk yarjejeniyar zaman lafiyar da ake aiwatarwa a Zirin Gazan.

Kawo yanzu Palasdinawa 47,460 ne aka kashe, tare da jikkata wasu  111,580 tun daga ranar 7 ga Oktoban 2023 da aka fara wannan yaki.

An kashe wasu kimanin 1,139 a Isra’ila a lokacin da kungiyar Palasdinawa ta Hamas ta kai hai a ranar, inda ta yi garkuwa da wasu kimanin 200, ciki har da baki ’yan kasashen waje.

‘Yan sandan Isra’ila sun kama wasa Palasdinawa 12 da ke murnar sako ’yan uwansu 110 daga gidajen yarin Isra’ila a wani bangare na yarjejeniyar zaman lafiya a Zirin Gazan.

Jami’an tsaron Isra’ilar sun tsare mutanen ne a yankin Gabashin Birnin Kudus saboda suka murnar sako Palasdinawa da Isra’ila ta tsare a gidajen yarinta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Isra ila Palasdinawa

এছাড়াও পড়ুন:

Kasancewar Zaman Lafiya Na Dogon Lokaci Tsakanin Sin Da Amurka Abu Ne Da Ya Zama Wajibi

Jakadan kasar Sin a Amurka Xie Feng ya bayyana a cikin wani jawabi ta bidiyo da ya gabatar ga taron kolin jagorancin Sin na Duke-UNC a ranar 28 ga watan Fabrairu cewa, kasancewar zaman lafiya mai dorewa tsakanin Sin da Amurka a duniya, abu ne da ya zama wajibi kuma nauyi ne dake kan wuyansu.

Xie Feng ya jaddada cewa, idan kasashen biyu suka dauki juna a matsayin abokan hamayya, kuma suka shiga mummunar gasa, kasashen za su yi rashin nasara, kuma duniya za ta sha wahala. Amma idan suka zama abokan huldar juna, da samun nasara tare, za su samu ci gaba tare, da kuma amfanar da duniya baki daya.

Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murnar Fara Azumin Ramadan An Samu Karuwar Jigilar Kayayyaki A Sabuwar Tashar Jigila Da Ta Hada Sin Da Kasashen Ketare

Ya ce babban abin sawa a gaba shi ne, Amurka ta mutunta ka’idar Sin daya tak, da daidaita batun yankin Taiwan yadda ya kamata, bisa kudurorin dake kunshe cikin takardu uku da Sin da Amurka suka amincewa, da adawa da “‘yancin kan Taiwan”, da daina kyautata alaka tsakanin Amurka da yankin Taiwan, da daina taimakawa yankin Taiwan fadada tasirinsa a wajen kasashen duniya, yin amfani da Taiwan don yaki da Sin zai kawo cikas ga kansa.

Kungiyoyin dalibai na jami’ar Duke da jami’ar North Carolina a Chapel Hill ne suka gudanar da taron kolin jagorancin Sin na Duke-UNC tare.(Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • MDD ta taya Musulmi murnar zuwan watan Ramadan
  • Lavrov Ya Yi Watsi Da Batun Aike Wa Da Dakarun Zaman Lafiya A Kasar Ukiraniya
  • Kasancewar Zaman Lafiya Na Dogon Lokaci Tsakanin Sin Da Amurka Abu Ne Da Ya Zama Wajibi
  • Hamas: Matakin Netanyahu na hana shigar kayan agaji a Gaza keta yarjejeniyar tsagaita wuta ne
  • Babban Sakataren MDD Ya Taya Musulmi Murnar Shiga Watan Ramadan
  • Hamas Ta Yi Watsi Da Shawarar Isra’ila Na Tsawaita Matakin Farko Na Tsagaita Wuta A Gaza
  • Al-Houthi : Isra’ila Na fakewa Da Goyan Bayan Amurka Tana Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza
  • An Yi Musayar Yawu A Tsakanin Shugabannin Kasashen Amurka Da Ukiraniya A Fadar White House
  • An kori ma’aikatan Microsoft saboda adawa da yahudawan sahyoniya
  • GORON JUMA’A