Abu Obeida ya sanar da shahadar shugaban Hamas Mohammad Deif
Published: 31st, January 2025 GMT
Dakarun Ezzeddine al-Qassam, reshen kungiyar gwagwarmayar Hamas masu dauke da makamai, sun sanar a jiya Alhamis shahadar babban kwamandan kungiyar Mohammad “Abu Khaled” Deif tare da wasu manyan kwamandoji da dama, a wani bangare na farmakin guguwar al-Aqsa.
Da yake magana a cikin wani faifan bidiyo da aka fitar ta kafar yada labaran soji ta al-Qassam, mai magana da yawun rundunar Abu Obeida ya ce, sanarwar ta zo ne “bayan kammala dukkan matakan da suka dace da kuma magance dukkan matsalolin tsaro da suke da alaka da yanayin da ake ciki, da kuma bayan gudanar da tantancewar da ta kamata.
“Muna sanar da al’ummarmu, da duk masu goyon bayan ‘yanci da tsayin daka a duniya, shahadar gungun manyan mayaka da kwamandojin rundunar soji ta al-Qassam Brigades,” in ji shi.
Daga cikin shugabannin da suka yi shahada har da Mohammad “Abu Khaled” Deif, kwamandan rundunar Al-Qassam Brigades, tare da Marwan “Abu Baraa” Issa, mataimakin kwamandan rundunar.
“Wannan shi ne abin da ya dace da kwamandan mu Mohammed Deif, Abu Khaled, wanda ya ke fafatwa da makiya sama da shekaru talatin, kuma yanzu ya shiga cikin tarihi na shahidai da suka sadaukar da rayuwarsu a tafarkin Allah da kare gaskiya a cewar Abu Ubaidah.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Hamas: Matakin Netenyahu Na Dakatar Da Shigar Kayan Agaji Cikin Gaza Keta Yarjejeniya Ne
Kungiyar Hamas ta yi kira ga masu shiga tsakani na kasa da kasa da su yi matsin lamba akan ‘yan mamaya su dakatar da azabatar da fiye da mutane miliyan daya da suke yi ta hanyar hana shigar da kayan agaji.
Kungiyar ta Hamas wacce ta fitar da sanarwa a yau Lahadi ta ce, matakin da Netanyahu ya dauka na dakatar shigar da kayan agaji cikin Gaza, wata tsokana ce, kuma laifin yaki ne sannan uwa uba keta yarjejeniyar datakar da wuta da musayar fursunoni ce.
Bugu da kari, kungiyar ta Hamas ta ce bukatar da Netanyahu ya gabatar na tsawaita zango na farko na yarjejeniyar, wani yunkuri ne na gujewa aiwatar da ita kanta yarjejeniyar.
Haka nan kuma Hamas ta bukaci Amurka da ta daina zama mai goyon bayan manufofin Netanyahu, tana mai jaddada cewa duk wani kokari na take hakkokin Falasdinawa ba zai haifar da da, mai ido ba.