Abu Obeida ya sanar da shahadar shugaban Hamas Mohammad Deif
Published: 31st, January 2025 GMT
Dakarun Ezzeddine al-Qassam, reshen kungiyar gwagwarmayar Hamas masu dauke da makamai, sun sanar a jiya Alhamis shahadar babban kwamandan kungiyar Mohammad “Abu Khaled” Deif tare da wasu manyan kwamandoji da dama, a wani bangare na farmakin guguwar al-Aqsa.
Da yake magana a cikin wani faifan bidiyo da aka fitar ta kafar yada labaran soji ta al-Qassam, mai magana da yawun rundunar Abu Obeida ya ce, sanarwar ta zo ne “bayan kammala dukkan matakan da suka dace da kuma magance dukkan matsalolin tsaro da suke da alaka da yanayin da ake ciki, da kuma bayan gudanar da tantancewar da ta kamata.
“Muna sanar da al’ummarmu, da duk masu goyon bayan ‘yanci da tsayin daka a duniya, shahadar gungun manyan mayaka da kwamandojin rundunar soji ta al-Qassam Brigades,” in ji shi.
Daga cikin shugabannin da suka yi shahada har da Mohammad “Abu Khaled” Deif, kwamandan rundunar Al-Qassam Brigades, tare da Marwan “Abu Baraa” Issa, mataimakin kwamandan rundunar.
“Wannan shi ne abin da ya dace da kwamandan mu Mohammed Deif, Abu Khaled, wanda ya ke fafatwa da makiya sama da shekaru talatin, kuma yanzu ya shiga cikin tarihi na shahidai da suka sadaukar da rayuwarsu a tafarkin Allah da kare gaskiya a cewar Abu Ubaidah.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna ya dakatar da basarake kan satar mutane da yankinsa
Gwamnan Jihar Edo, Monday Okpebholo, ya dakatar da basaraken yankin Masarautar Uwano Kingdom, Dakta George Oshiapi Egabor, nan take saboda matsalar yi garkuwa da mutane a yankin.
Dakta George Oshiapi Egabor shi ne Okumagbe na Masarautar Uwano da ke Agenebode a Karamar Hukumar Etsako ta jihar.
Kakakin gwamnan, Fred Itua, a cikin wata sanarwa, ya bayyana cewa an dakatar da basaraken ne har sai abin da hali ya yi, saboda yawan samun kashe-kashe da kuma garkuwa da mutane a masarautarsa a baya-bayan nan.
Ya ce tuni jami’an tsaro suka tsare sakataren basaraken, Cif Peter Omiogbemhi, sakamakon wani sabon hari a da ya yi ajalin wani bafade, Cif John Ikhamate. Mutanen da aka kashe a Binuwai sun ƙaru zuwa 72 An tsinci gawar saurayi da buduwarsa a tuɓe a cikin daƙi A baya-bayan nan an samu yawaitar garkuwa da mutane a yankin, wanda ya haddasa ƙone ofishin ’yan sandan da ke kula da yankin. Daga cikin waɗanda aka yi garkuwa da su har da wasu malaman coci guda uku da aka yi aka yi awon gaba da su a wani coci, inda daga baya aka sako biyu bayan an biya kudin fansa, na ukun kuma aka kashe.