Iran Za Ta Kara Bunkasa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Kasashen Eurasia
Published: 31st, January 2025 GMT
Mataimakin shugaban kasar Iran na farko Mohammad Reza Aref ya jaddada muhimmancin karfafa hadin gwiwar tattalin arziki da kasuwanci da kasar Kazakhstan a wata ganawa da firaministan kasar Kazakhstan Olzhas Bektenov.
A yayin taron na ranar Alhamis, Aref ya bayyana bukatar samar da karin kwamitocin hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu.
Bayan goron gayyata day a samu a hukumance daga Bektenov, mataimakin shugaban kasar Iran na farko ya isa kasar Kazakhstan a ranar Alhamis domin halartar taron koli na shugabannin gwamnatoci mambobi a kungiyar tattalin arzikin Eurasia (EAEU) da taron Almaty Digital Summit 2025, wanda aka shirya gudanarwa daga ranar 31 ga watan Janairu zuwa 1 ga Fabrairu.
Iran wadda a baya-bayan nan ta samu matsayin mamba mai sanya ido a kungiyar EAEU, na neman kara zurfafa alaka da kungiyar a bangarori na tattalin arziki.
EAEU, wacce aka kafa a cikin 2015, ta ƙunshi Rasha, Belarus, Kazakhstan, Kyrgyzstan, da Armeniya, kuma tana da niyyar habaka haɗin gwiwar tattalin arziki ta hanyar hadaddiyar kasuwa don musayar kayayyaki, ayyuka a bangaren gine-gine da sauransu.
Aref ya jaddada dangantakar al’adu tsakanin Iran da Kazakhstan, yana mai nuni da yuwuwar fadada hadin gwiwa a fannin yawon bude ido da mu’amalar al’adu.
Ya kuma mika goron gayyata ga Bektenov don halartar taron kolin Caspian mai zuwa, wanda aka shirya gudanarwa a Tehran a karshen watan Fabrairu.
Da yake bayyana ci gaban da Iran ta samu a fannin fasahar sadarwa, Aref ya bayyana shirye-shiryen Tehran na raba gwaninta kan fasahohin da ke tasowa tare da kasashe makwabta.
A nasa bangaren, Bektenov ya taya Iran murnar zagayowar ranar juyin juya halin Musulunci tare da jaddada aniyar kasar Kazakhstan na karfafa alakar kasashen biyu ta hanyar inganta kwamitocin hadin gwiwa.
Iran da Kazakhstan a tarihi sun kulla alaka mai karfi, tare da moriyar makamashi, sufuri, da kasuwanci.
Matsakaicin yanayin ƙasa na Iran yana ba Kazakhstan damar shiga tashar jiragen ruwa na kudanci, yana sauƙaƙe hanyoyin kasuwanci kamar Hanyar Sufuri ta Arewa-Kudanci. Sabanin haka, zama memba na EAEU na Kazakhstan yana baiwa Iran kofar shiga kasuwannin tsakiyar Asiya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Kazakhstan
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Zama Zakara A Damben Gargajiya Ta 2025 UWW Wanda Aka Gudanar A Kasar Albaniya
Tawagar yan wasan Damben Gargariya ta kasar Iran sun zama zakara a wasan damben da ya gudana a birnin Tirana babban birnin kasar Albaniya a makon da ya gabata, inda suka tashi da lambobin yabo 6 wadanda suka hada da zinari 4 azurfa da tagulla.
Wannan nasara da ta maida kasar a matsayin zakara a wannan wata a fagen kasa da kasa. Tawagar damben gargaji ta kasar Iran ita ce zakara a gasar damben na wannan shekara ta 2025 haka ita ce zakara a gasar shekara ta 2024.
An gudanar da gasar ne a ranakun 27-28 na watan Fabrayrun wannan shekara, wato 2025UWW, wanda ya jawo hankalin masu shaawar wasan a duniya.
Daga cikin yan wasan da suka sami lambar zinari sun hada har da Ali Momini mai nauyin (57) Rahman Amouzad (65) Kamran Ghasempour da kuma Amir Hussain Zare.(125).
Sai kuma mai lambar Azurfa, wato Erfan Alizadeh (97). Younes Emami (74kg) ya sami tagulla. Iran ta sami maki 97 sai kuma kasar Japan wacce ta zo na biyu da maki 93.