Leadership News Hausa:
2025-03-03@17:03:20 GMT

Gwamnan Gombe Ya Jaddada Aniyarsa Ta Inganta Fannin Shari’a

Published: 31st, January 2025 GMT

Gwamnan Gombe Ya Jaddada Aniyarsa Ta Inganta Fannin Shari’a

A nata jawabin, babbar mai shari’a ta Jihar Gombe, Mai Shari’a Halima S. Mohammed, ta bayyana cewa an shigar da kararraki guda 616 wadanda suka shafi manya da kananan laifuka da kuma cin zarafi a babbar kotun jihar, daga cikinsu 555 an kammala shari’arsu, inda wadanda suka rage ba su kai 70 ba.

Ta bayyana godiya ga Gwamna Yahaya bisa ba da kwangilar biliyoyin naira na gina babbar sakatariyar kotun da sauran taimako da dama.

Babban Lauyan gwamnatin jihar kuma Kwamishinan Shari’a, Barrister Zubairu Muhammad Umar, ya bayyana cewa gwamnatin Yahaya ta taka rawar gani wajen samun nasarorin da ma’aikatarsa ta samu a yunkurinta na ciyar da sashin shari’a gaba.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun hallaka mutum 6 a ƙauyukan Kebbi

’Yan bindiga sun kai hari ƙauyukan Bagiza da Rausa Kade a Ƙaramar Hukumar Arewa, Jihar Kebbi, inda suka kashe mutum shida a makon da ya gabata.

Maharan sun kashe mutum biyar a Rausa Kade, sannan suka hallaka ɗaya a Bagiza yayin harin da suka kai domin satar shanu.

Matata ta taɓa kawo min ƙarar Akpabio — Mijin Natasha Girke-girken Azumi: Yadda ake yin Tsiren Dankali

Wannan ta’addanci ya jefa mazauna yankin cikin tsananin fargaba.

Gwamna Nasir Idris ya bayar da tabbacin inganta a tsaro jihar.

Ganin yadda mutane ke cikin tsoro, Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya kai ziyarar jaje ƙauyukan a ranar Asabar.

Ya tabbatarwa da al’ummar yankin cewa gwamnati na aiki tuƙuru domin shawo kan matsalar tsaro, musamman a yankin Kebbi ta Kudu.

Gwamnan ya bayyana cewa mafi yawan hare-haren da ake fuskanta a Kebbi na zuwa ne daga maƙwabtan jihohi.

“Tun daga lokacin da muka hau mulki, muna ɗaukar matakan da suka dace domin magance matsalar tsaro, kuma muna samun ci gaba.

“Rashin ɗaukar matakin gaggawa daga jami’an tsaro a wasu maƙwabtan jihohi yana bai wa ’yan bindiga damar kutsowa cikin yankunanmu suna kai hari,” in ji Gwamnan.

Ya buƙaci jami’an tsaro da su ƙara ƙaimi domin kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

A yayin ziyarar, Gwamna Nasir Idris ya bayar da tallafin miliyan 10 ga iyalan waɗanda aka kashe.

Haka kuma, ya bayar da umarnin gina Masallacin Juma’a da kuma bohol guda biyu da ke amfani da hasken rana a ƙauyen Rausa Kade.

Shugaban Ƙaramar Hukumar Arewa, Hon. Sani Aliyu Tela, ya jinjina wa Gwamnan bisa wannan kulawa.

Ya bayyana cewa harin ya faru ne a daren Alhamis, inda ’yan bindiga suka kai farmaki domin satar dabbobi.

“Sun kashe mutum biyar a Rausa Kade, suka harbi mutum ɗaya a Bagiza. Mun yaba da kulawar da kake ba mu,” in ji shi.

Jama’a dai na fatan matakan da gwamnati ke ɗauka za su kawo ƙarshen hare-haren da suka addabi yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda ’yan bindiga suka sace ɗalibai 4 a Jami’ar Tarayya ta Dutsinma
  • ’Yan bindiga sun hallaka mutum 6 a ƙauyukan Kebbi
  • Hukumar NOA Ta Bukaci Al’umma Su Kara Hakuri Da Kaunar Juna
  • Fasinjoji 12 sun ƙone ƙurmus a hatsarin mota a Edo
  • Yan Ta’adda Sun kashe Sojojin Sa Kai Na Basij Biyu A Yankin Kudu Maso Gabacin Kasar Iran
  • Shugabar Tanzaniya Ta Yaba Da Yadda Ake Ci Gaba Da Samun Karuwar Jigilar Kayayyaki A Tashar Tanga Da Sin Ta Inganta
  • ‘Yansanda Na Farautar Wadanda Suka Kashe Dalibi A Katsina
  • MohBad: Nurse Za Ta Fuskanci Shari’a, Sannan Kotu Ta Wanke Naira Marley, Sam Larry Da PrimeBoy
  • MDD Ta Bayyana Cewa Yara Fiye Da 100,000 Ne Suka Ka Yi Rijistan Fara Karatu A Makarantun Gaza Na Sabuwar Shekarar Karatu
  • Kungiyar Kare Hakkin Bil’adama ta ‘Euro-Med Monitor’ Ta Ce Ta Sami Shaidu Wadanda Suka Tabbatar Da Cewa HKI Tana Azabtar Da Fulasdinwa