Sarkin ya yi addu’a Allah ya jiƙansa, ya gafarta masa, kuma ya bai wa iyalansa haƙuri.

.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Zaria

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda za ku yi rajista a shafin Itikafi a Saudiyya

Mahukuntan Saudiyya sun buɗe shafi na musamman domin yin rajista ga masu sha’awar yin ibadar Itikifa a watan Ramadan da muke ciki a ƙasar.

A ranar Lahadi, 1 ga watan Ramadana ne aka sanar da buɗe shafin ga masu sha’awar yin Itikafi ’yan asalin ƙasar da kuma baƙi.

Sanarwar ta bayyana ka’idojin da masu sha’awar za su cika domin samun gudanar da ibadar a kwanaki 10 ma ƙarshen watan Ramadan a masallatan Haramin Makkah da Madina da sauransu masallatan ƙasar.

Bayanan da ake buƙata sun hada da:

Ɓacewar bindigogi 4,000: Sakaci ne dalili —’Yan sanda NAJERIYA A YAU: Yadda za ku yi girke-girken azumi da kuɗi kaɗan MDD ta taya Musulmi murnar zuwan watan Ramadan

1- Ƙasar mutum: Ta asali ko inda yake zama. Sanarwar ta bayyana cewa wajibi ne mai yin rajistar ya kasance ɗan ƙasar Saudiyya ko ya mallaki takardar iznin zama a can.

2- Wurin yin rajista: Wajibi ne mutum ya kasance a Saudiyya a lokacin da zai yi rajista, domin wanda ke wajen ƙasar ba zai iya shiga shafin ba.

3- Shekaru: Wajibi ne mai yin Itikafi ya shekarunsa su kai aƙalla 18.

4- Yanayin lafiya: An buƙatar ya kasance cikin ƙoshin lafiya ta yadda zai iya gudanar da ibada ba tare da wahala ba. Za a yi wa mutum gwajin duk wasu cututtuka masu tsanani. Idan mutum na buƙatar kulawa ta musamman, wajibi ne ya bayyana a yayin yin rajista.

5- Wa’adin Itikafi: Dole ne mutum ya bai ka’idar kwanakin da ya ɗiba na Itikafi. Lokacin ya fara ne daga ranar 20 ga watan Ramadana zuwa bayan Sallar Isha’ ta ranar jajibirin Ƙaramar Sallah.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda za ku yi rajista a shafin Itikafi a Saudiyya
  • Matata ta taɓa kawo min ƙarar Akpabio — Mijin Natasha
  • Sarkin Sasa ya rasu bayan shafe shekaru 125 a doron ƙasa
  • Yadda ake ‘Spring rolls’
  • Bayan Kwana 22, Tsohon Shugaban NYSC Tsiga Ya Kuɓuta A Hannun Ƴan Bindiga
  • An ga watan Ramadan a Najeriya — Sarkin Musulmi
  • An ga watan Ramadan a Najeriya —Sarkin Musulmi
  • Hukumar Alhazai Ta Kaduna Ta Nemi Goyon Bayan Sarkin Zazzau Don Nasarar Aikin Hajjin Bana
  • Ka Cire Sarkin Kano Bayero Daga Fadar Nasarawa – Gwamnatin Kano Ga Tinubu
  • Cibiyar bincike ta nemi a tabbatar da dokar kare haƙƙin mata a Arewa